< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
De Salomon. O Dieu, confie au roi le soin d'exercer en ton nom la justice. Et donne au fils du roi ton esprit d'équité!
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Qu'il juge ton peuple avec justice, Et tes humbles serviteurs avec droiture!
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Que les montagnes et les coteaux Procurent au peuple les fruits de la paix, Sous le règne de la justice!
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Il fera droit aux opprimés de son peuple; Il portera secours aux enfants du pauvre. Et il écrasera l'oppresseur.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
On te craindra tant que durera le soleil, Tant que luira la lune, d'âge en âge.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Le roi sera semblable à la pluie Qui tombe sur la prairie fraîchement coupée. Semblable à une ondée qui arrose la terre.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Sous son règne, le juste prospérera Au sein d'une paix profonde, tant que la lune répandra sa clarté.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Il dominera d'une mer à l'autre, Depuis l'Euphrate jusqu'aux extrémités de la terre.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Devant lui se courberont les habitants du désert, Et ses ennemis lécheront la poussière.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Les rois de Tarsis et des îles lui offriront des présents; Les rois de Saba et de Séba lui apporteront leurs tributs.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Tous les rois se prosterneront devant lui; Toutes les nations le serviront.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Car il délivrera le malheureux qui l'implore, Et l'affligé qui n'a pas d'appui.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Il aura pitié du faible et de l'indigent; Il sauvera l'âme des malheureux.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Il rachètera leur âme de l'oppression et de la violence. Et leur sang aura un grand prix à ses yeux.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Que le roi vive et qu'on lui donne de l'or de Saba! Qu'on prie pour lui, en tout temps. Qu'on le bénisse chaque jour!
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Que les blés abondent dans le pays. Sur le sommet des montagnes! Que leurs épis ondoient comme le Liban! Que la population des villes fleurisse comme l'herbe de la terre!
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Que son nom subsiste à toujours! Que son nom se perpétue tant que brillera le soleil! Que l'on se bénisse mutuellement en son nom; Que toutes les nations le proclament heureux!
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
BÉNI SOIT l'Éternel Dieu, le Dieu d'Israël, Qui seul accomplit des oeuvres merveilleuses!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Béni soit a jamais son nom glorieux. Et que toute la terre soit remplie de sa gloire! Amen! Amen!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Fin des prières de David, fils d'Isaï.

< Zabura 72 >