< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Par Salomon. Dieu, donne au roi ta justice; ta justice au fils royal.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Il jugera ton peuple avec droiture, et vos pauvres avec justice.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Les montagnes apporteront la prospérité au peuple. Les collines apportent le fruit de la justice.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Il jugera les pauvres du peuple. Il sauvera les enfants des nécessiteux, et brisera l'oppresseur en morceaux.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Ils te craindront tant que durera le soleil; et aussi longtemps que la lune, à travers toutes les générations.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Il descendra comme la pluie sur l'herbe fauchée, comme les averses qui arrosent la terre.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
En ses jours, les justes fleuriront, et l'abondance de la paix, jusqu'à ce que la lune ne soit plus.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Il dominera aussi d'une mer à l'autre, depuis le fleuve jusqu'aux extrémités de la terre.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Ceux qui habitent dans le désert se prosterneront devant lui. Ses ennemis lécheront la poussière.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Les rois de Tarsis et des îles apporteront un tribut. Les rois de Saba et de Seba offriront des cadeaux.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Oui, tous les rois se prosterneront devant lui. Toutes les nations le serviront.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Car il délivre l'indigent quand il crie; le pauvre, qui n'a pas d'aide.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Il aura pitié des pauvres et des indigents. Il sauvera les âmes des nécessiteux.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Il rachètera leur âme de l'oppression et de la violence. Leur sang sera précieux à ses yeux.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Il vivra, et l'or de Saba lui sera donné. Les hommes prieront pour lui continuellement. Ils le béniront toute la journée.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Il y aura abondance de grains dans tout le pays. Son fruit se balance comme le Liban. Qu'il s'épanouisse, qu'il prospère comme l'herbe des champs.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Son nom subsiste à jamais. Son nom perdure aussi longtemps que le soleil. Les hommes seront bénis par lui. Toutes les nations le diront béni.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Loué soit le Dieu Yahvé, le Dieu d'Israël, qui seul fait des merveilles.
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Que son nom glorieux soit béni à jamais! Que la terre entière soit remplie de sa gloire! Amen et amen.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Ainsi s'achèventles prières de David, fils de Jessé.

< Zabura 72 >