< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Of Solomon. Give the king, O God, your own spirit of justice your spirit of right to the son of the king,
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
that with right he may judge your people, and your downtrodden ones with justice.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
May the mountains bear weal for the people, and the hills yield fruits of justice.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
The weak may he help to their rights, may he save the sons of the needy and crush the oppressor in pieces.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
May he live as long as the sun, while the moon shines – for ages and ages.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
May he be like the rain on the meadow, like showers that water the earth.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
In his days may justice flourish, and welfare abound, till the moon be no more.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
May he reign from ocean to ocean, from the river to the ends of the earth.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
May his foes bow down before him, his enemies lick the dust.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
May tribute be rendered by kings of the isles and of Tarshish; may gifts be brought by the kings of Sheba and Seba.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
May all kings fall prostrate before him, and all nations yield him their service.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
For he saves the poor when he cries, the helpless and the downtrodden.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
He pities the weak and the poor, he saves the lives of the poor.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
He redeems them from wrong and from violence, for dear is their blood in his sight.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Long may he live; and may gold of Sheba be given him; prayer, too, be made for him ceaselessly, all the day long may men bless him.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
May the land have abundance of corn, to the tops of the hills may it wave. May the fruit thereof flourish like Lebanon, may men spring from the city like grass of the earth.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
May his name be blessed forever, may his fame endure as the sun. May all nations envy his blessedness, all tribes of the earth call him happy.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Blest be the Lord God, Israel’s God, who alone does wonders;
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
And blest be forever his glorious name. Let all the earth be filled with his glory. Amen and Amen.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Here end the prayers of David, son of Jesse.

< Zabura 72 >