< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
David psalmus filiorum Ionadab et priorum captivorum in te Domine speravi non confundar in aeternum
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
in iustitia tua libera me et eripe me inclina ad me aurem tuam et salva me
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
esto mihi in Deum protectorem et in locum munitum ut salvum me facias quoniam firmamentum meum et refugium meum es tu
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Deus meus eripe me de manu peccatoris de manu contra legem agentis et iniqui
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
quoniam tu es patientia mea Domine Domine spes mea a iuventute mea
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
in te confirmatus sum ex utero de ventre matris meae tu es protector meus in te cantatio mea semper
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
tamquam prodigium factus sum multis et tu adiutor fortis
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
repleatur os meum laude ut cantem gloriam tuam tota die magnitudinem tuam
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
non proicias me in tempore senectutis cum deficiet virtus mea ne derelinquas me
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
quia dixerunt inimici mei mihi et qui custodiebant animam meam consilium fecerunt in unum
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
dicentes Deus dereliquit eum persequimini et conprehendite eum quia non est qui eripiat
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Deus ne elongeris a me Deus meus in adiutorium meum respice
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
confundantur et deficiant detrahentes animae meae operiantur confusione et pudore qui quaerunt mala mihi
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
ego autem semper sperabo et adiciam super omnem laudem tuam
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
os meum adnuntiabit iustitiam tuam tota die salutem tuam quoniam non cognovi litteraturam
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
introibo in potentiam Domini Domine memorabor iustitiae tuae solius
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Deus docuisti me ex iuventute mea et usque nunc pronuntiabo mirabilia tua
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
et usque in senectam et senium Deus ne derelinquas me donec adnuntiem brachium tuum generationi omni quae ventura est potentiam tuam
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
et iustitiam tuam Deus usque in altissima quae fecisti magnalia Deus quis similis tibi
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
quantas ostendisti mihi tribulationes multas et malas et conversus vivificasti me et de abyssis terrae iterum reduxisti me
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
multiplicasti magnificentiam tuam et conversus consolatus es me
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
nam et ego confitebor tibi in vasis psalmi veritatem tuam Deus psallam tibi in cithara Sanctus Israhel
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
exultabunt labia mea cum cantavero tibi et anima mea quam redemisti
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
sed et lingua mea tota die meditabitur iustitiam tuam cum confusi et reveriti fuerint qui quaerunt mala mihi