< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
Psalmus David, Filiorum Ionadab, et priorum captivorum. In te Domine speravi, non confundar in æternum:
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
in iustitia tua libera me, et eripe me. Inclina ad me aurem tuam, et salva me.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Esto mihi in Deum protectorem, et in locum munitum: ut salvum me facias. Quoniam firmamentum meum, et refugium meum es tu.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Deus meus eripe me de manu peccatoris, et de manu contra legem agentis et iniqui:
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Quoniam tu es patientia mea Domine: Domine spes mea a iuventute mea.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
In te confirmatus sum ex utero: de ventre matris meæ tu es protector meus: In te cantatio mea semper:
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
tamquam prodigium factus sum multis: et tu adiutor fortis.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Repleatur os meum laude, ut cantem gloriam tuam: tota die magnitudinem tuam.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Ne proiicias me in tempore senectutis: cum defecerit virtus mea, ne derelinquas me.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Quia dixerunt inimici mei mihi: et qui custodiebant animam meam, consilium fecerunt in unum,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Dicentes: Deus dereliquit eum, persequimini, et comprehendite eum: quia non est qui eripiat.
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Deus ne elongeris a me: Deus meus in auxilium meum respice.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Confundantur, et deficiant detrahentes animæ meæ: operiantur confusione, et pudore qui quærunt mala mihi.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Ego autem semper sperabo: et adiiciam super omnem laudem tuam.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Os meum annuntiabit iustitiam tuam: tota die salutare tuum. Quoniam non cognovi litteraturam,
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
introibo in potentias Domini: Domine, memorabor iustitiæ tuæ solius.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Deus docuisti me a iuventute mea: et usque nunc pronuntiabo mirabilia tua.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Et usque in senectam et senium: Deus ne derelinquas me, Donec annunciem brachium tuum generationi omni, quæ ventura est: Potentiam tuam,
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
et iustitiam tuam Deus usque in altissima, quæ fecisti magnalia: Deus quis similis tibi?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Quantas ostendisti mihi tribulationes multas, et malas: et conversus vivificasti me: et de abyssis terræ iterum reduxisti me:
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Multiplicasti magnificentiam tuam: et conversus consolatus es me.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Nam et ego confitebor tibi in vasis psalmi veritatem tuam: Deus psallam tibi in cithara, Sanctus Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
Exultabunt labia mea cum cantavero tibi: et anima mea, quam redemisti.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Sed et lingua mea tota die meditabitur iustitiam tuam: cum confusi et reveriti fuerint qui quærunt mala mihi.

< Zabura 71 >