< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
J'ai cherché en toi mon refuge, ô Éternel; Que mon espoir ne soit jamais déçu!
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Dans ta justice, délivre-moi, retire-moi du danger; Incline ton oreille vers moi, et sauve-moi!
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Sois mon rocher, la retraite Où je puisse me réfugier en tout temps! Tu as donné des ordres pour que je sois sauvé; Car tu es mon rocher et ma forteresse.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Mon Dieu, délivre-moi des mains du méchant, Des mains de l'homme inique et de l'oppresseur!
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Car tu es mon espérance, ô Seigneur, Éternel! C'est en toi que je me confie depuis ma jeunesse.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
Je me suis appuyé sur toi dès ma naissance; C'est toi qui m'as tiré du sein de ma mère! Tu es l'objet de mes louanges en tout temps.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
Je suis, pour plusieurs, un sujet d'étonnement; Mais toi, tu es ma forte citadelle.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Que ma bouche soit pleine de ta louange. Et qu'elle te glorifie chaque jour!»
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Ne me rejette pas au temps de ma vieillesse; Quand ma force s'en va, ne m'abandonne point!
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Car mes ennemis parlent de moi; Ceux qui guettent ma vie conspirent ensemble,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Disant: «Dieu l'a abandonné; Poursuivez-le, saisissez-le; Car il n'y a personne pour le délivrer!»
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Dieu! Ne t'éloigne pas de moi! Mon Dieu, accours à mon aide!
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Que ceux qui en veulent à ma vie Rougissent de honte et qu'ils périssent! Que ceux qui cherchent ma perte Soient couverts d'opprobre et de confusion!
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Mais moi, j'espérerai en tout temps, Et je te louerai toujours davantage.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Ma bouche célébrera chaque jour Ta justice et tes délivrances. Sans jamais parvenir à énumérer tes bienfaits.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
Je raconterai partout tes grandes oeuvres, Seigneur, Éternel! C'est ta justice seule que je célébrerai.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Dieu, tu m'as instruit dès ma jeunesse. Et jusqu'à ce jour j'ai fait connaître tes oeuvres merveilleuses,
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
C'est pourquoi, jusqu'à la vieillesse. Jusqu'à la blanche vieillesse, Dieu, ne m'abandonne pas, Afin que je révèle la vigueur de ton bras à la génération nouvelle, Et ta puissance à tous ceux qui naîtront!
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Ta justice, ô Dieu, atteint jusqu'au ciel! Tu as accompli de grandes oeuvres. Dieu, qui est semblable à toi?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Après m'avoir fait passer par des détresses Et des maux sans nombre. Tu m'as de nouveau rendu la vie, Et tu m'as fait remonter des abîmes de la terre!
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Tu accroîtras ma grandeur, Et tu me consoleras encore.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Aussi, je te célébrerai sur les cordes de la lyre; Je chanterai ta fidélité, ô mon Dieu! Je psalmodierai en ton honneur sur la harpe, ô Saint d'Israël!
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
Mes lèvres, et mon âme que tu as rachetée, Entonneront des chants de joie. Quand je psalmodierai à ta gloire.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Ma langue aussi, chaque jour, redira ta justice; Car ils seront confus, ils rougiront. Ceux qui souhaitent ma ruine!