< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
Eternel! je me suis retiré vers toi, fais que je ne sois jamais confus.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Délivre-moi par ta justice, et me garantis: incline ton oreille vers moi, et me mets en sûreté.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Sois-moi pour un rocher de retraite, afin que je m'y puisse toujours retirer; tu as donné ordre de me mettre en sûreté; car tu es mon rocher, et ma forteresse.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Mon Dieu! délivre-moi de la main du méchant, de la main du pervers, et de l'oppresseur.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Car tu es mon attente, Seigneur Eternel! [et] ma confiance dès ma jeunesse.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
J'ai été appuyé sur toi dès le ventre [de ma mère]; c'est toi qui m'as tiré hors des entrailles de ma mère; tu es le sujet continuel de mes louanges.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
J'ai été à plusieurs comme un monstre; mais tu es ma forte retraite.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Que ma bouche soit remplie de ta louange, et de ta magnificence chaque jour.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Ne me rejette point au temps de ma vieillesse; ne m'abandonne point maintenant que ma force est consumée.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Car mes ennemis ont parlé de moi, et ceux qui épient mon âme ont pris conseil ensemble;
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Disant: Dieu l'a abandonné; poursuivez-le, et le saisissez; car il n'y a personne qui le délivre.
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Ô Dieu! ne t'éloigne point de moi; mon Dieu hâte-toi de venir à mon secours.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Que ceux qui sont ennemis de mon âme soient honteux et défaits; et que ceux qui cherchent mon mal soient enveloppés d'opprobre et de honte.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Mais moi je vivrai toujours en espérance en toi, et je te louerai tous les jours davantage.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Ma bouche racontera chaque jour ta justice, [et] ta délivrance, bien que je n'en sache point le nombre.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
Je marcherai par la force du Seigneur Eternel; je raconterai ta seule justice.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Ô Dieu! tu m'as enseigné dès ma jeunesse, et j'ai annoncé jusques à présent tes merveilles.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
[Je les ai annoncées] jusqu’à la vieillesse, même jusques à la vieillesse toute blanche; ô Dieu! ne m'abandonne point jusqu’à ce que j'aie annoncé ton bras à cette génération, et ta puissance à tous ceux qui viendront après.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Car ta justice, ô Dieu! est haut élevée, parce que tu as fait de grandes choses. Ô Dieu qui est semblable à toi?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Qui m'ayant fait voir plusieurs détresses et plusieurs maux, m'as de nouveau rendu la vie, et m'as fait remonter hors des abîmes de la terre?
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Tu accroîtras ma grandeur, et tu me consoleras encore.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Aussi, mon Dieu! je te célébrerai pour l'amour de ta vérité avec l'instrument de la musette; ô Saint d'Israël, je te psalmodierai avec la harpe.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
Mes lèvres et mon âme, que tu auras rachetée, chanteront de joie, quand je te psalmodierai.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Ma langue aussi discourra chaque jour de ta justice, parce que ceux qui cherchent mon mal seront honteux et rougiront.

< Zabura 71 >