< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
Yahweh, en toi j'ai placé mon refuge; que jamais je ne sois confondu!
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Dans ta justice délivre-moi et sauve-moi! Incline vers moi ton oreille et secours-moi!
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Sois pour moi un rocher inaccessible, où je puisse toujours me retirer. Tu as commandé de me sauver, car tu es mon rocher et ma forteresse.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Mon Dieu, délivre-moi de la main du méchant, de la main de l'homme inique et cruel.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Car tu es mon espérance, Seigneur Yahweh, l'objet de ma confiance depuis ma jeunesse.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
C'est sur toi que je m'appuie depuis ma naissance, toi qui m'as fait sortir du sein maternel: tu es ma louange à jamais!
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
Je suis pour la foule comme un prodige, mais toi, tu es mon puissant refuge.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Que ma bouche soit pleine de ta louange, que chaque jour elle exalte ta magnificence!
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Ne me rejette pas aux jours de ma vieillesse; au déclin de mes forces ne m'abandonne pas.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Car mes ennemis conspirent contre moi, et ceux qui épient mon âme se concertent entre eux,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
disant: " Dieu l'a abandonné! Poursuivez-le; saisissez-le; il n'y a personne pour le défendre! "
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
O Dieu, ne t'éloigne pas de moi; mon Dieu, hâte-toi de me secourir!
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Qu'ils soient confus, qu'ils périssent, ceux qui en veulent à ma vie! Qu'ils soient couverts de honte et d'opprobre, ceux qui cherchent ma perte!
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Pour moi, j'espérerai toujours; à toutes tes louanges, j'en ajouterai de nouvelles.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Ma bouche publiera ta justice, tout le jour tes faveurs; car je n'en connais pas le nombre.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
Je dirai tes œuvres puissantes, Seigneur Yahweh; je rappellerai ta justice, la tienne seule.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
O Dieu, tu m'as instruit dès ma jeunesse, et jusqu'à ce jour je proclame tes merveilles.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Encore jusqu'à la vieillesse et aux cheveux blancs, O Dieu, ne m'abandonne pas, afin que je fasse connaître ta force à la génération présente, ta puissance à la génération future.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Ta justice, ô Dieu, atteint jusqu'au ciel, toi qui accomplis de grandes choses, — ô Dieu, qui est semblable à toi? —
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
toi qui nous a causé des épreuves nombreuses et terribles. Mais tu nous rendras la vie, et des abîmes de la terre tu nous feras remonter.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Tu relèveras ma grandeur et de nouveau tu me consoleras.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Et je louerai au son du luth, je chanterai ta fidélité, ô mon Dieu, je te célébrerai avec la harpe, Saint d'Israël.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
L'allégresse sera sur mes lèvres, quand je te chanterai, et dans mon âme, que tu as délivrée.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Et ma langue chaque jour publiera ta justice, car ils seront confus et ils rougiront, ceux qui cherchent ma perte.

< Zabura 71 >