< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
En toi, Yahvé, je trouve refuge. Ne me laisse jamais être déçu.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Délivre-moi dans ta justice, et sauve-moi. Prêtez l'oreille et sauvez-moi.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Sois pour moi un rocher de refuge où je puisse toujours aller. Donne l'ordre de me sauver, car tu es mon rocher et ma forteresse.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Sauve-moi, mon Dieu, de la main des méchants, de la main de l'homme injuste et cruel.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Car tu es mon espérance, Seigneur Yahvé, ma confiance de ma jeunesse.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
J'ai compté sur toi depuis le ventre de ma mère. Tu es celui qui m'a sorti du ventre de ma mère. Je vous louerai toujours.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
Je suis une merveille pour beaucoup, mais tu es mon fort refuge.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Ma bouche sera remplie de tes louanges, avec votre honneur toute la journée.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Ne me rejette pas dans ma vieillesse. Ne m'abandonne pas quand mes forces faiblissent.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Car mes ennemis parlent de moi. Ceux qui veillent sur mon âme conspirent ensemble,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
disant: « Dieu l'a abandonné. Poursuivez-le et prenez-le, car personne ne le sauvera. »
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Dieu, ne t'éloigne pas de moi. Mon Dieu, dépêchez-vous de m'aider.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Que mes accusateurs soient déçus et consumés. Qu'ils soient couverts d'opprobre et de mépris ceux qui veulent me nuire.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Mais j'espère toujours, et s'ajoutera à toutes vos louanges.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Ma bouche racontera ta justice, et de votre salut toute la journée, bien que je n'en connaisse pas toute la mesure.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
Je viendrai avec les actes puissants du Seigneur Yahvé. Je ferai mention de ta justice, même de la tienne seule.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Dieu, tu m'as enseigné dès ma jeunesse. Jusqu'à présent, j'ai déclaré tes merveilles.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Oui, même quand je serai vieux et que j'aurai des cheveux blancs, Dieu, ne m'abandonne pas, jusqu'à ce que je déclare ta force à la prochaine génération, ta puissance à tous ceux qui viendront.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Dieu, ta justice atteint aussi les cieux. Vous avez fait de grandes choses. Dieu, qui est comme toi?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Toi, qui nous as fait connaître de nombreuses et amères souffrances, tu me laisseras vivre. Tu nous feras remonter des profondeurs de la terre.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Augmentez mon honneur et me réconforter à nouveau.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Je te louerai aussi avec la harpe pour ta fidélité, mon Dieu. Je te chante des louanges avec la lyre, Saint d'Israël.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
Mes lèvres crient de joie! Mon âme, que tu as rachetée, te chante des louanges!
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Ma langue parlera aussi de ta justice tout le jour, car ils sont déçus, et ils sont confus, qui veulent me faire du mal.