< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
In thee, O LORD, do I put my trust: let me never be ashamed.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Deliver me in thy righteousness, and rescue me: bow down thine ear unto me, and save me.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Be thou to me a rock of habitation, whereunto I may continually resort: thou hast given commandment to save me; for thou art my rock and my fortress.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Rescue me, O my God, out of the hand of the wicked, out of the hand of the unrighteous and cruel man.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For thou art my hope, O Lord GOD: [thou art] my trust from my youth.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
By thee have I been holden up from the womb: thou art he that took me out of my mother’s bowels: my praise shall be continually of thee.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
I am as a wonder unto many; but thou art my strong refuge.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
My mouth shall be filled with thy praise, and with thy honour all the day.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Cast me not off in the time of old age; forsake me not when my strength faileth.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For mine enemies speak concerning me; and they that watch for my soul take counsel together,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Saying, God hath forsaken him: pursue and take him; for there is none to deliver.
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
O God, be not far from me: O my God, make haste to help me.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Let them be ashamed [and] consumed that are adversaries to my soul; let them be covered with reproach and dishonour that seek my hurt.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
But I will hope continually, and will praise thee yet more and more.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
My mouth shall tell of thy righteousness, [and] of thy salvation all the day; for I know not the numbers [thereof].
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will come with the mighty acts of the Lord GOD: I will make mention of thy righteousness, even of thine only.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
O God, thou hast taught me from my youth; and hitherto have I declared thy wondrous works.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Yea, even when I am old and grayheaded, O God, forsake me not; until I have declared thy strength unto [the next] generation, thy might to every one that is to come.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Thy righteousness also, O God, is very high; thou who hast done great things, O God, who is like unto thee?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Thou, which hast shewed us many and sore troubles, shalt quicken us again, and shalt bring us up again from the depths of the earth.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Increase thou my greatness, and turn again and comfort me.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
I will also praise thee with the psaltery, [even] thy truth, O my God: unto thee will I sing praises with the harp, O thou Holy One of Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
My lips shall greatly rejoice when I sing praises unto thee; and my soul, which thou hast redeemed.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
My tongue also shall talk of thy righteousness all the day long: for they are ashamed, for they are confounded, that seek my hurt.