< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
In thee, O LORD! do I put my trust! Let me never be put to shame!
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
In thy goodness deliver and rescue me; Incline thine ear to me, and save me!
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Be thou the rock of my abode, where I may continually resort! Thou hast granted me deliverance; For thou art my rock and my fortress!
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Save me, O my God! from the hand of the wicked, -From the hand of the unjust and cruel!
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For thou art my hope, O Lord Jehovah! Thou hast been my trust from my youth!
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
Upon thee have I leaned from my birth; From my earliest breath thou hast been my support; My song hath been continually of thee!
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
I am a wonder to many, But thou art my strong refuge.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Let my mouth be filled with thy praise; Yea, all the day long, with thy glory.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Cast me not off in mine old age; Forsake me not, When my strength faileth!
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For my enemies speak against me, And they who lay wait for my life consult together:
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
“God,” say they, “hath forsaken him; Pursue and seize him; for he hath none to deliver him!”
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
O God! be not far from me! Come speedily to mine aid, O my God!
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Let them perish with shame who are my enemies; Let them be covered with contempt and dishonor who seek my hurt!
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
But I will hope continually; I shall yet praise thee more and more.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
My mouth shall speak of thy goodness, —Of thy sure protection all the day long; For thy mercies are more than I can number.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will celebrate thy mighty deeds, O Lord Jehovah! I will make mention of thy goodness, of thine only!
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
O God! thou hast taught me from my youth, And thus far have I declared thy wondrous deeds;
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
And now, when I am old and gray-headed, O God! forsake me not, Until I make known thine arm to the next generation, -Thy mighty power to all that are to come!
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
For thy goodness, O God! reacheth to the heavens; Wonderful things doest thou! O God! who is like unto thee?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Thou hast suffered us to see great and grievous troubles; Thou wilt again give us life, And wilt bring us back from the depths of the earth!
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Thou wilt increase my greatness; Thou wilt again comfort me!
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Then will I praise thee with the psaltery; Even thy faithfulness, O my God! To thee will I sing with the harp, O Holy One of Israel!
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
My lips shall rejoice, when I sing to thee; And my soul, which thou hast redeemed from death;
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
My tongue also shall continually speak of thy righteousness: For all who seek my hurt are brought to shame and confounded.

< Zabura 71 >