< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
In Thee, O LORD, have I taken refuge; let me never be ashamed.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Deliver me in Thy righteousness, and rescue me; incline Thine ear unto me, and save me.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Be Thou to me a sheltering rock, whereunto I may continually resort, which Thou hast appointed to save me; for Thou art my rock and my fortress.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
O my God, rescue me out of the hand of the wicked, out of the grasp of the unrighteous and ruthless man.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For Thou art my hope; O Lord GOD, my trust from my youth.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
Upon Thee have I stayed myself from birth; Thou art He that took me out of my mother's womb; my praise is continually of Thee.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
I am as a wonder unto many; but Thou art my strong refuge.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
My mouth shall be filled with Thy praise, and with Thy glory all the day.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Cast me not off in the time of old age; when my strength faileth, forsake me not.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For mine enemies speak concerning me, and they that watch for my soul take counsel together,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Saying: 'God hath forsaken him; pursue and take him; for there is none to deliver.'
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
O God, be not far from me; O my God, make haste to help me.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Let them be ashamed and consumed that are adversaries to my soul; let them be covered with reproach and confusion that seek my hurt.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
But as for me, I will hope continually, and will praise Thee yet more and more.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
My mouth shall tell of Thy righteousness, and of Thy salvation all the day; for I know not the numbers thereof.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will come with Thy mighty acts, O Lord GOD; I will make mention of Thy righteousness, even of Thine only.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
O God, Thou hast taught me from my youth; and until now do I declare Thy wondrous works.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
And even unto old age and hoary hairs, O God, forsake me not; until I have declared Thy strength unto the next generation, Thy might to every one that is to come.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Thy righteousness also, O God, which reacheth unto high heaven; Thou who hast done great things, O God, who is like unto Thee?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Thou, who hast made me to see many and sore troubles, wilt quicken me again, and bring me up again from the depths of the earth.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Thou wilt increase my greatness, and turn and comfort me.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
I also will give thanks unto Thee with the psaltery, even unto Thy truth, O my God; I will sing praises unto Thee with the harp, O Thou Holy One of Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
My lips shall greatly rejoice when I sing praises unto Thee; and my soul, which Thou hast redeemed.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
My tongue also shall tell of Thy righteousness all the day; for they are ashamed, for they are abashed, that seek my hurt.

< Zabura 71 >