< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
In thee, O Lord, I trust: let me neuer be ashamed.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Rescue mee and deliuer me in thy righteousnes: incline thine eare vnto me and saue me.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Be thou my strong rocke, whereunto I may alway resort: thou hast giuen commandement to saue me: for thou art my rocke, and my fortresse.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Deliuer mee, O my God, out of the hande of the wicked: out of the hande of the euill and cruell man.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For thou art mine hope, O Lord God, euen my trust from my youth.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
Vpon thee haue I beene stayed from the wombe: thou art he that tooke me out of my mothers bowels: my praise shalbe alwaies of thee.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
I am become as it were a monster vnto many: but thou art my sure trust.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Let my mouth be filled with thy praise, and with thy glory euery day.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Cast mee not off in the time of age: forsake me not when my strength faileth.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For mine enemies speake of mee, and they that lay waite for my soule, take their counsell together,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Saying, God hath forsaken him: pursue and take him, for there is none to deliuer him.
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Goe not farre from me, O God: my God, haste thee to helpe me.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Let them be confounded and consumed that are against my soule: let them be couered with reproofe and confusion, that seeke mine hurt.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
But I will waite continually, and will praise thee more and more.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
My mouth shall daily rehearse thy righteousnesse, and thy saluation: for I knowe not the nomber.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will goe forwarde in the strength of the Lord God, and will make mention of thy righteousnesse, euen of thine onely.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
O God, thou hast taught me from my youth euen vntill nowe: therefore will I tell of thy wonderous workes,
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Yea, euen vnto mine olde age and graie head, O God: forsake me not, vntill I haue declared thine arme vnto this generation, and thy power to all them, that shall come.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
And thy righteousnes, O God, I wil exalt on high: for thou hast done great thinges: O God, who is like vnto thee!
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Which hast shewed me great troubles and aduersities, but thou wilt returne, and reuiue me, and wilt come againe, and take mee vp from the depth of the earth.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Thou wilt increase mine honour, and returne and comfort me.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Therefore will I praise thee for thy faithfulnesse, O God, vpon instrument and viole: vnto thee will I sing vpon the harpe, O Holy one of Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
My lippes will reioyce when I sing vnto thee, and my soule, which thou hast deliuered.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
My tongue also shall talke of thy righteousnesse daily: for they are confounded and brought vnto shame, that seeke mine hurt.