< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
Lord, you are the one who keeps me safe; please don't disappoint me.
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Save me, rescue me, because you always do what is right.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Please listen to me, and save me. Be my rock of protection where I can always go and hide. You gave the command to save me; for you are my rock and fortress.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
My God, rescue me from the power of the wicked, from the clutches of those who are evil and brutal.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For you, Lord God, are my hope. You are the one I have trusted since I was young.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
I have depended on you since birth; you have taken care of me from my mother's womb. That's why I'm always praising you!
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
My life has been like a miracle to many people, for you have been my powerful protector.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
All day long I am full of praise for you, telling how wonderful you are!
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Don't reject me now I'm getting old. When my strength is gone, please don't abandon me.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For my enemies are talking about me; those who want to kill me are plotting together.
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
They say, “God has given up on him. Let's go after him because there's no one to save him.”
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
God, please don't stay away from me. My God, hurry to help me!
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Defeat my accusers, get rid of them! May those who want to cause me trouble be covered with shame and disgrace!
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
As for me, I will go on hoping in you, and I will praise you more and more.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
I will talk about your goodness and your salvation every day, even though it's more than I can understand.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will come and explain what the Lord has done. I will remind people that you alone do what is right.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
God, you have taught me since I was young, and I still tell others about all the wonderful things you do.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Even though I'm old and gray, please don't abandon me, God. Let me tell the new generation about your power. Let me explain to all who are to come the great things you do.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
God, your trustworthy and true nature is higher than the highest heaven! You have done incredible things! God, who is like you?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
You had me face many troubles and plenty of misery, but you will bring me back to life; you will rise me up from the depths of the earth.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
You will give me even greater prestige, and you will make me happy again.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Then I will praise you on the harp for your trustworthiness, my God. I will sing praises to you on the lyre, Holy One of Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
I will shout for joy as I sing praises to you, for you have redeemed me.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
All day long I will tell about all the good things you have done, for those who tried to cause me misery have been disgraced and humiliated.