< Zabura 71 >
1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
A psalm for David. Of the sons of Jonadab, and the former captives. In thee, O Lord, I have hoped, let me never be put to confusion:
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Deliver me in thy justice, and rescue me. Incline thy ear unto me, and save me.
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Be thou unto me a God, a protector, and a place of strength: that thou mayst make me safe. For thou art my firmament and my refuge.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Deliver me, O my God, out of the hand of the sinner, and out of the hand of the transgressor of the law and of the unjust.
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
For thou art my patience, O Lord: my hope, O Lord, from my youth;
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
By thee have I been confirmed from the womb: from my mother’s womb thou art my protector. Of thee shall I continually sing:
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
I run become unto many as a wonder, but thou art a strong helper.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Let my mouth be filled with praise, that I may sing thy glory; thy greatness all the day long.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Cast me not off in the time of old age: when my strength shall fail, do not thou forsake me.
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
For my enemies have spoken against me; and they that watched my soul have consulted together,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
Saying: God hath forsaken him: pursue and take him, for there is none to deliver him.
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
O God, be not thou far from me: O my God, make haste to my help.
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Let them be confounded and come to nothing that detract my soul; let them be covered with confusion and shame that seek my hurt.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
But I will always hope; and will add to all thy praise.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
My mouth shall shew forth thy justice; thy salvation all the day long. Because I have not known learning,
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
I will enter into the powers of the Lord: O Lord, I will be mindful of thy justice alone.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Thou hast taught me, O God, from my youth: and till now I will declare thy wonderful works.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
And unto old age and grey hairs: O God, forsake me not, Until I shew forth thy arm to all the generation that is to come: Thy power,
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
And thy justice, O God, even to the highest great things thou hast done: O God, who is like to thee?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
How great troubles hast thou shewn me, many and grievous: and turning thou hast brought me to life, and hast brought me back again from the depths of the earth:
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Thou hast multiplied thy magnificence; and turning to me thou hast comforted me.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
For I will also confess to thee thy truth with the instruments of psaltery: O God, I will sing to thee with the harp, thou holy one of Israel.
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
My lips shall greatly rejoice, when I shall sing to thee; and my soul which thou hast redeemed.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Yea and my tongue shall meditate on thy justice all the day; when they shall be confounded and put to shame that seek evils to me.