< Zabura 70 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
Para el director del coro. Un salmo de David. Para un memorial. Oh, Dios, ¡sálvame! ¡Apresúrate a ayudarme!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Por favor, vence y humilla a los que tratan de matarme. Haz que los que me hieren retrocedan con deshonra.
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Que los que se burlan de mi se horroricen de su derrota.
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Pero que Sean felices todos los que vienen a ti; que los que aman tu salvación siempre digan: “¡Cuán grande es Dios!”
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
En lo que a mi concierne, soy un pobre y menesteroso. ¡Apresúrate, oh Dios, a ayudarme! ¡No esperes más!

< Zabura 70 >