< Zabura 70 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
Til sangmesteren; av David; til ihukommelse. Gud, kom for å utfri mig! Herre, skynd dig å hjelpe mig!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
La dem som står mig efter livet, bli til skam og spott! La dem som ønsker min ulykke, vike tilbake og bli til skamme!
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
La dem som sier: Ha, ha, vende tilbake for sin skjensels skyld!
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
La dem fryde og glede sig i dig, alle de som søker dig, og la dem som elsker din frelse, alltid si: Høilovet være Gud!
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
For jeg er elendig og fattig; Gud, skynd dig til mig! Du er min hjelp og min frelser; Herre, dryg ikke!