< Zabura 70 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
Au chef des chantres. De David. Pour la Commémoration. Consens, ô Dieu, à me sauver; Eternel, hâte-toi de me porter secours.
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Qu’ils soient confondus et couverts de honte, ceux qui attentent à ma vie: qu’ils lâchent pied et reculent, en rougissant, ceux qui souhaitent mon malheur!
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Qu’ils s’en retournent, punis par leur honte, ceux qui disent de moi: "Ha! Ha!"
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Mais qu’ils jubilent et se réjouissent en toi, tous ceux qui te recherchent! Qu’ils disent constamment: "Dieu est grand", ceux qui aiment ta protection!
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
Quant à moi, pauvre et malheureux, ô Dieu, hâte-toi en ma faveur; tu es mon aide et ma sauvegarde: Eternel, n’attends pas trop longtemps.