< Zabura 70 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
Au chef de musique. De David; pour faire souvenir. Hâte-toi, ô Dieu, de me délivrer! [hâte-toi], ô Éternel, de me secourir!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Que ceux qui cherchent ma vie soient honteux et confondus; qu’ils se retirent en arrière et soient confus, ceux qui prennent plaisir à mon malheur;
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Qu’ils retournent en arrière à cause de leur honte, ceux qui disent: Ha ha! ha ha!
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Que tous ceux qui te cherchent s’égaient et se réjouissent en toi; et que ceux qui aiment ton salut disent continuellement: Magnifié soit Dieu!
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
Et moi, je suis affligé et pauvre; ô Dieu, hâte-toi vers moi! Tu es mon secours et celui qui me délivre; Éternel, ne tarde pas!

< Zabura 70 >