< Zabura 70 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
God, please save me! Yahweh, come quickly to help me!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Humble those who are happy about my troubles/difficulties, and cause them to be disgraced/ashamed. Chase away those who are trying to kill me.
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
I hope/desire that you will cause them to become dismayed and ashamed [because you have defeated them].
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
[But] I hope/desire that all those who go to [worship] you will be very joyful [DOU]. I want those who love you because you saved them to shout repeatedly [HYP], “God is great!”
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
As for me, I am poor and needy [DOU]; [so] God, come quickly to help me! Yahweh, you are the one who saves and helps me, [so please] come quickly!

< Zabura 70 >