< Zabura 70 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
“To the chief musician, by David, to bring to remembrance.” O God, [arise] to deliver me; O Lord, make haste to help me.
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Let those that seek after my life be made ashamed and put to the blush: let those that desire my unhappiness be turned backward and put to confusion.
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Let them be turned backward in consequence of their shame, that say, Aha, aha.
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Let all those that seek thee be glad and rejoice in thee: and let such as love thy salvation say continually, God is great.
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
But I am poor and needy, O God: come hastily unto me; my help and my deliverer art thou: O Lord, do not delay.