< Zabura 70 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
For the choirmaster. Of David. To bring remembrance. Make haste, O God, to deliver me! Hurry, O LORD, to help me!
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
May those who seek my life be ashamed and confounded; may those who wish me harm be repelled and humiliated.
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
May those who say, “Aha, aha!” retreat because of their shame.
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
May all who seek You rejoice and be glad in You; may those who love Your salvation always say, “Let God be magnified!”
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
But I am poor and needy; hurry to me, O God. You are my help and my deliverer; O LORD, do not delay.

< Zabura 70 >