< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Oh SEÑOR mi Dios, puse mi fe en ti; sácame de las manos de todos los que me persiguen y hazme libre;
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Para que no destruyan mi alma como un león, y me despedacen, sin quien haya quien me salve.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Oh Señor mi Dios, si he hecho esto; si mis manos han hecho algo mal;
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
Si he devuelto el mal al que estaba en paz conmigo, o si he tomado algo del que estuvo en mi contra sin causa;
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Deja que mi enemigo vaya tras mi alma y la tome; deja que mi vida sea arrastrada en la tierra y mi honor en el polvo. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Levántate, Señor, en tu ira; se levantado contra mis enemigos; Y despierta en favor mío el juicio que mandaste.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
La reunión de las naciones te rodeará; toma tu trono, entonces, sobre ellos, en lo alto.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
El Señor juzgará a los pueblos; júzgame, oh Señor, a causa de mi justicia, y conforme a mi integridad.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Ojalá el mal del malvado llegue a su fin, pero de fortaleza a los justos: porque el Dios de justicia prueba las mentes y los corazones de los hombres.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Mi protección está en Dios, que es el salvador de los rectos de corazón.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Dios es un juez justo, y está enojado con los malvados todos los días.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Si el hombre no se aparta de su maldad, afilará su espada; su arco está preparado y listo.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Él preparó para él los instrumentos de la muerte; él hace sus flechas llamas de fuego.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Miren al malvado; concibió maldad, se preñó de iniquidad, y dio a luz mentira.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Hizo un hoyo en lo profundo de la tierra, y está cayendo en el hoyo que hizo.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Su maldad volverá a él, y su comportamiento violento caerá sobre su cabeza.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
Alabaré a Jehová por su justicia; cantaré una canción al nombre del Señor Altísimo.

< Zabura 7 >