< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Lamento che Davide rivolse al Signore per le parole di Cus il Beniaminita. Signore, mio Dio, in te mi rifugio: salvami e liberami da chi mi perseguita,
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
perché non mi sbrani come un leone, non mi sbrani senza che alcuno mi salvi.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Signore mio Dio, se così ho agito: se c'è iniquità sulle mie mani,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
se ho ripagato il mio amico con il male, se a torto ho spogliato i miei avversari,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
il nemico m'insegua e mi raggiunga, calpesti a terra la mia vita e trascini nella polvere il mio onore.
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Sorgi, Signore, nel tuo sdegno, levati contro il furore dei nemici, alzati per il giudizio che hai stabilito.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
L'assemblea dei popoli ti circondi: dall'alto volgiti contro di essa.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Il Signore decide la causa dei popoli: giudicami, Signore, secondo la mia giustizia, secondo la mia innocenza, o Altissimo.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Poni fine al male degli empi; rafforza l'uomo retto, tu che provi mente e cuore, Dio giusto.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
La mia difesa è nel Signore, egli salva i retti di cuore.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Dio è giudice giusto, ogni giorno si accende il suo sdegno.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Non torna forse ad affilare la spada, a tendere e puntare il suo arco?
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Si prepara strumenti di morte, arroventa le sue frecce.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Ecco, l'empio produce ingiustizia, concepisce malizia, partorisce menzogna.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Egli scava un pozzo profondo e cade nella fossa che ha fatto;
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
la sua malizia ricade sul suo capo, la sua violenza gli piomba sulla testa.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
Loderò il Signore per la sua giustizia e canterò il nome di Dio, l'Altissimo.

< Zabura 7 >