< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Éternel, mon Dieu, je me retire vers toi; sauve-moi de tous ceux qui me poursuivent, et délivre-moi!
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
De peur qu'ils ne me déchirent comme un lion, et ne me mettent en pièces sans que personne me délivre.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Éternel, mon Dieu, si j'ai fait cela, s'il y a de l'iniquité dans mes mains;
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
Si j'ai rendu le mal à celui qui était en paix avec moi, et si j'ai dépouillé celui qui m'opprimait sans cause;
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Que l'ennemi me poursuive et qu'il m'atteigne; qu'il foule à terre ma vie et couche ma gloire dans la poussière! (Sélah, pause)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Lève-toi, Éternel, dans ta colère! Élève-toi contre les fureurs de mes ennemis; réveille-toi, viens à moi; accomplis le jugement que tu as ordonné.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Que l'assemblée des peuples t'environne; remonte au-dessus d'elle vers les lieux élevés!
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
L'Éternel juge les peuples. Juge-moi, Éternel, selon ma justice, selon l'intégrité qui est en moi.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Que la malice des méchants prenne fin, et affermis le juste, toi qui sondes les cœurs et les reins, ô Dieu juste!
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Dieu est mon bouclier; il délivre ceux qui ont le cœur droit.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Dieu est un juste juge, un Dieu qui s'indigne en tout temps.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Si le méchant ne se convertit, Dieu affile son épée; il a bandé son arc, et il l'ajuste.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Il prépare contre lui des armes mortelles, il apprête des flèches ardentes.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Voici, le méchant est en travail pour enfanter le mal; il a conçu le crime, mais il n'enfante que mensonge.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Il a creusé un trou profond; mais il tombera dans la fosse qu'il a faite.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Sa malice retournera sur sa tête, sa violence retombera sur son front.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
Je célébrerai l'Éternel à cause de sa justice; je chanterai le nom de l'Éternel, le Très-Haut.

< Zabura 7 >