< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Siggajon de David, qu'il chanta à l'Eternel touchant l'affaire de Cus Benjamite. Eternel mon Dieu! je me suis retiré vers toi; délivre-moi de tous ceux qui me poursuivent, et garantis-moi.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
De peur qu'il ne me déchire comme un lion, me mettant en pièces, sans qu'il y ait personne qui me délivre.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Eternel mon Dieu! si j'ai commis une telle action, s'il y a de l'iniquité dans mes mains;
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
Si j'ai récompensé de mal celui qui avait la paix avec moi, et si je n'ai pas garanti celui qui m'opprimait à tort;
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Que l'ennemi me poursuive, et qu'il m'atteigne; qu'il foule ma vie en terre, et qu'il loge ma gloire dans la poudre! (Sélah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Lève-toi, ô Eternel! en ta colère, parais pour arrêter les fureurs de mes ennemis, et te réveille pour moi; tu as ordonné le droit.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Que l'assemblée des peuples t'environne, et toi tourne-toi vers elle en un lieu éminent.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Que l'Eternel juge les peuples; fais moi droit, ô Eternel! selon ma justice, et selon mon intégrité, qui est en moi.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Que la malice des méchants prenne fin, et affermis le juste, toi, dis-je, qui sondes les cœurs et les reins; ô Dieu juste!
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Mon bouclier est en Dieu, qui délivre ceux qui sont droits de cœur.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Dieu fait droit au juste, et le [Dieu] Fort s'irrite tous les jours.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Si [le méchant] ne se convertit, Dieu aiguisera son épée; il a bandé son arc et l'a ajusté.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Et il a préparé contre lui des armes mortelles; il mettra en œuvre ses flèches contre les ardents persécuteurs.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Voici [le méchant] travaille pour enfanter l'outrage, et il a conçu le travail: mais il enfantera une chose qui le trompera.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Il a fait une fosse, il l'a creusée: mais il est tombé dans la fosse qu'il a faite.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Son travail retournera sur sa tête, et sa violence lui descendra sur le sommet.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
Je célébrerai l'Eternel selon sa justice, et je psalmodierai le Nom de l’Eternel souverain.

< Zabura 7 >