< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
'The Erring One,' by David, that he sung to Jehovah concerning the words of Cush a Benjamite. O Jehovah, my God, in Thee I have trusted, Save me from all my pursuers, and deliver me.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest he tear as a lion my soul, Rending, and there is no deliverer.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O Jehovah, my God, if I have done this, If there is iniquity in my hands,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have done my well-wisher evil, And draw mine adversary without cause,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
An enemy pursueth my soul, and overtaketh, And treadeth down to the earth my life, And my honour placeth in the dust. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Rise, O Jehovah, in Thine anger, Be lifted up at the wrath of mine adversaries, And awake Thou for me: Judgment Thou hast commanded:
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
And a company of peoples compass Thee, And over it on high turn Thou back,
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Jehovah doth judge the peoples; Judge me, O Jehovah, According to my righteousness, And according to mine integrity on me,
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Let, I pray Thee be ended the evil of the wicked, And establish Thou the righteous, And a trier of hearts and reins is the righteous God.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield [is] on God, Saviour of the upright in heart!
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God [is] a righteous judge, And He is not angry at all times.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If [one] turn not, His sword he sharpeneth, His bow he hath trodden — He prepareth it,
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Yea, for him He hath prepared Instruments of death, His arrows for burning pursuers He maketh.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Lo, he travaileth [with] iniquity, And he hath conceived perverseness, And hath brought forth falsehood.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
A pit he hath prepared, and he diggeth it, And he falleth into a ditch he maketh.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Return doth his perverseness on his head, And on his crown his violence cometh down.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I thank Jehovah, According to His righteousness, And praise the name of Jehovah Most High!

< Zabura 7 >