< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
A musical composition of David, which he sang to Yahweh concerning the words of Cush the Benjamite. Yahweh my God, I take refuge in you! Save me from all who chase me, and rescue me.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Otherwise, they will rip me apart like a lion, tearing me in pieces with no one else able to bring me to safety.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Yahweh my God, if I have done this, and there is guilt on my hands—
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
if I have done evil to him who was at peace with me, or senselessly harmed my enemy without cause, then hear my words.
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Then let my enemy pursue my life and overtake me; let him trample my life to the ground and lay my honor in the dust. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, Yahweh, in your anger; stand up against the rage of my enemies; wake up for my sake and carry out the righteous decrees that you have commanded for them.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
The countries are assembled all around you; take once more your rightful place over them.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Yahweh, judge the nations; vindicate me, Yahweh, because I am righteous and innocent, Most High.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
May the evil deeds of the wicked come to an end, but establish the righteous people, righteous God, you who examine hearts and minds.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield comes from God, the one who saves the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a righteous judge, a God who is indignant each day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If a person does not repent, God will sharpen his sword and will prepare his bow for battle.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He prepares to use weapons against him; he makes his arrows flaming shafts.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Think about the one who is pregnant with wickedness, who conceives destructive plans, who gives birth to harmful lies.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He digs a pit and hollows it out and then falls into the hole he has made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His own destructive plans return to his own head, for his violence comes down on his own head.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will give thanks to Yahweh for his justice; I will sing praise to Yahweh Most High.