< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Ode of David: which he sang unto Yahweh, on account of the words of Cush the Benjamite. O Yahweh my God, in thee, have I sought refuge, —Save me from all my pursuers, and deliver me:
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest one tear, as a lion, my soul, —and there be no deliverer to rescue.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O Yahweh my God, If I have done this, If there hath been perversity in my hands:
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have requited my friend with wrong, —or have oppressed mine adversary without need,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Let an enemy pursue my soul, and overtake it, that he may tread down, to the earth, my life, —and, mine honour—in the dust, he may cause to dwell. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Rise! Yahweh! in thine anger, Lift thyself up, because of the haughty outbursts of mine adversaries, Stir up for me the justice thou hast commanded:
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
When, the assembly of peoples, gather round thee, then, above it—on high, do thou return!
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Yahweh, will judge the peoples, —Do me justice, O Yahweh, according to my righteousness, and according to mine integrity upon me,
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Let the wrong of the lawless, I pray thee, come to an end, and establish thou him that is righteous, —for, a trier of hearts and reins, is God the righteous one.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield, is held by God, who is ready to save the upright in heart:
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
A God to vindicate the righteous, —And yet a God to be indignant throughout every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If he turn not, his sword, will he whet, —his bow, hath he bent, and made ready:
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
But, for himself, hath he made ready the weapons so deadly, His arrows, he, so fiery, would make:
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Lo! he gendereth trouble, and conceiveth mischief, but giveth birth to a disappointment:
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
A pit, he cut out, and digged it, and then fell into the ditch he had made:
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His mischief, turneth back, on his own head, —and, on his own crown, his violence, descendeth.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will praise Yahweh according to his righteousness, —and will praise in song the Name of Yahweh Most High.

< Zabura 7 >