< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
A Shiggaion of David, which he sang to the Lord about Cush, the Benjamite. Lord my God, I take refuge in you. Deliver me, save me from all who pursue me;
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
or like lions they will tear me to pieces, and rend me, past hope of rescue.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Lord, my God, if my life has been such if my hands have been stained with guilt,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
if friends I paid back with evil, if I plundered my foes without cause,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
may the enemy chase and find me, trample my life to the ground, my honor leave in the dirt! (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, Lord, in anger, against my foes rise in fury. Awake for my help: let justice be done.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Gather the nations about you, and sit on your lofty throne,
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
as the Lord, the judge of the peoples. Judge me, Lord, in my innocence and according to my integrity.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Put an end to the wrong of the wicked, protect the righteous. Searcher of hearts and minds, righteous God.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
God is my shield: he saves the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a just judge, constant in righteous anger.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
He will sharpen his sword without fail, his bow is bent and ready,
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
his deadly weapons are ready, his arrows he makes of flame.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
The enemy who conceives evil; pregnant with mischief, giving birth to lies,
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
a pit they have made and dug; but into the hole that they made they will fall.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
On their own heads their mischief comes back; on their own skulls their violence comes down.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will give thanks to the Lord for his justice, and sing to the name of the Lord Most High.