< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Adonai, my God, I take refuge in you. Save me from all those who pursue me, and deliver me,
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
lest they tear apart my soul like a lion, ripping it in pieces, while there is no one to deliver.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Adonai, my God, if I have done this, if there is iniquity in my hands,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
if I have rewarded evil to him who was at peace with me (yes, if I have delivered him who without cause was my adversary),
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
let the enemy pursue my soul, and overtake it; yes, let him tread my life down to the earth, and lay my glory in the dust. (Selah) ·contemplation with musical interlude·.
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, Adonai, in your anger. Lift up yourself against the rage of my adversaries. Awake for me. You have enjoined judgment.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Let the congregation of the peoples surround you. Rule over them on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Adonai administers judgment to the peoples. Judge me, Adonai, according to my righteousness, and to my integrity that is in me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Oh let the wickedness of the wicked come to an end, but establish the upright; their minds and hearts are searched by the righteous God.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield is with God, who saves the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a righteous judge, yes, a God who has indignation every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If a man does not relent, he will sharpen his sword; he has bent and strung his bow.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He has also prepared for himself the instruments of death. He makes ready his flaming arrows.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold, he travails with vain striving of iniquity. Yes, he has conceived mischief, and brought out falsehood.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He has dug a hole, and has fallen into the pit which he made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
The trouble he causes shall teshuvah ·completely return· to his own head. His violence shall come down on the crown of his own head.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will yadah ·extend hands in thankful praise· to Adonai according to his righteousness, and will make zahmar ·musical praise· to the name of Adonai Most High.

< Zabura 7 >