< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
“A psalm of David, which he sang to Jehovah, on account of the reproaches of Cush the Benjamite.” O Jehovah, my God! to thee do I look for help; Save me from them that persecute me, and deliver me!
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest mine enemy tear me like a lion; Lest he rend me in pieces, while there is none to help.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O Jehovah, my God! if I have done this, —If there be iniquity upon my hands,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have rendered evil to my friend, Or have despoiled him that without cause is mine enemy, —
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Let my adversary pursue and take me; Let him trample me to the ground, And lay me prostrate in the dust! (Pause)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, O LORD! in thine anger; Lift thyself up against the rage of mine enemies; Awake for me, ordain judgment!
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Let the assembly of the nations compass thee about, And on their account return to the height!
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
The LORD judgeth the nations; Judge me, O LORD! according to my righteousness, And requite me according to my integrity!
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Oh, let the wickedness of the wicked be at an end; But establish the righteous! For the righteous God trieth the heart and the reins.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield is with God, Who saveth the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a righteous judge, And a God who is angry every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If he do not desist, He sharpeneth his sword; He bendeth his bow, and maketh it ready;
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He prepareth for him the instruments of death; He shooteth his burning arrows.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold, he travailed with iniquity, And conceived mischief, But hath brought forth disappointment!
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He made a pit and digged it. And is fallen into the ditch which he made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His mischief returneth upon his own head, And his violence cometh down upon his own skull.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will praise the LORD according to his righteousness; I will sing praise to the name of the LORD most high.

< Zabura 7 >