< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
[A meditation by David, which he sang to YHWH, concerning the words of Cush, the Benjamite.] YHWH, my God, I take refuge in you. Save me from all those who pursue me, and deliver me,
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
lest they tear apart my soul like a lion, ripping it in pieces, while there is none to deliver.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
YHWH, my God, if I have done this, if there is iniquity in my hands,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
if I have rewarded evil to him who was at peace with me, or oppressed my enemy without cause,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
let the enemy pursue my soul, and overtake it; yes, let him tread my life down to the earth, and lay my glory in the dust. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, YHWH, in your anger. Lift up yourself against the rage of my adversaries. Awake, my God; you have appointed judgment.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
And let the congregation of the peoples surround you, and rule over them on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
YHWH administers judgment to the peoples. Judge me, YHWH, according to my righteousness, and to my integrity that is in me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Oh let the wickedness of the wicked come to an end, but establish the righteous. The righteous God tests hearts and minds.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield is with God, who saves the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a righteous judge, yes, a God who has indignation every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If a man doesn't relent, he will sharpen his sword; he has bent and strung his bow.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He has also prepared for himself deadly weapons. He makes ready his flaming arrows.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Look, he travails with iniquity. Yes, he has conceived mischief, and brought forth falsehood.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He has dug a hole, and has fallen into the pit which he made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
The trouble he causes shall return to his own head, and his violence shall come down on the crown of his own head.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will give thanks to YHWH according to his righteousness, and will sing praise to the name of YHWH Most High.

< Zabura 7 >