< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
A SHIGGAION OF DAVID, THAT HE SUNG TO YHWH CONCERNING THE WORDS OF CUSH, A BENJAMITE. O YHWH, my God, in You I have trusted, Save me from all my pursuers, and deliver me.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest he tear my soul as a lion, Tearing, and there is no deliverer.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O YHWH, my God, if I have done this, If there is iniquity in my hands,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have done my well-wisher evil, And draw my adversary without cause,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
[Then] an enemy pursues my soul, and overtakes, And treads down my life to the earth, And places my glory in the dust. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Rise, O YHWH, in Your anger, Be lifted up at the wrath of my adversaries, And awake Yourself for me: You have commanded judgment.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
And a congregation of peoples surround You, And over it turn back on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
YHWH judges the peoples; Judge me, O YHWH, According to my righteousness, And according to my integrity [that is] on me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Please let the evil of the wicked be ended, And establish the righteous, And a trier of hearts and reins is the righteous God.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My shield [is] on God, Savior of the upright in heart!
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God [is] judging right, And He is not angry at all times.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If [one] does not turn, He sharpens His sword, He has bent His bow [and] He prepares it,
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Indeed, He has prepared for Himself Instruments of death, He makes His arrows for burning pursuers.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold, he travails [with] iniquity, And he has conceived perverseness, And has brought forth falsehood.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He has prepared a pit, and he digs it, And he falls into a ditch he makes.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His perverseness returns on his head, And his violence comes down on his crown.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I thank YHWH, According to His righteousness, And I praise the Name of YHWH Most High!