< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
A Psalm of David, which he sang to the Lord because of the words of Chusi the Benjamite. O Lord my God, in you have I trusted: save me from all them that persecute me, and deliver me.
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest at any time [the enemy] seize my soul as a lion, while there is none to ransom, nor to save.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O Lord my God, if I have done this; (if there is unrighteousness in my hands; )
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
if I have requited with evil those who requited me [with good]; may I then perish empty by means of my enemies.
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Let the enemy persecute my soul, an take it; and let him trample my life on the ground, and lay my glory in the dust. (Pause)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, O Lord, in your wrath; be exalted in the utmost boundaries of mine enemies: awake, O Lord my God, according to the decree which you did command.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
And the congregation of the nations shall compass you: and for this cause do you return on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
The Lord shall judge the nations: judge me, O Lord, according to my righteousness, and according to my innocence that is in me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Oh let the wickedness of sinners come to an end; and [then] you shall direct the righteous, O God that search the hearts and reins.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My help is righteous, [coming] from God who saves the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a righteous judge, and strong, and patient, not inflicting vengeance every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If you will not repent, he will furbish his sword; he has bent his bow, and made it ready.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
And on it he has fitted the instruments of death; he has completed his arrows for the raging ones.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold, he has travailed with unrighteousness, he has conceived trouble, and brought forth iniquity.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He has opened a pit, and dug it up, and he shall fall into the ditch which he has made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His trouble shall return on his own head, and his unrighteousness shall come down on his own crown.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will give thanks to the Lord according to his righteousness; I will sing to the name of the Lord most high.