< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
A psalm (shiggaion) of David, which he sang to the Lord concerning Cush, from the tribe of Benjamin. Lord my God, you are my protection. Save me from those who persecute me; please rescue me!
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Otherwise they will tear me apart like a lion, ripping me to pieces with no one to save me.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
If I have done what I'm accused of, if my hands are guilty,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have paid back a friend with evil, if I have robbed my enemy for no reason,
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Then let my enemies chase me down; let them trample me in the dust and drag my reputation through the dirt. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Stand up, Lord, in your anger, rise up against the fury of my enemies; wake up, Lord, and bring me justice!
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Bring together the nations before you; rule them from your throne on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
The Lord judges all people. Defend me, Lord, because I do what is right, because of my integrity.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Please bring an end to the evil done by the wicked; vindicate those who do good, for you are the God of right who examines hearts and minds.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
The Most High God is my defense, the one who saves those who live right.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God is a fair judge who is always hostile to evil.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If people do not change their minds, he will sharpen his sword. He has bent and strung his bow.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He has prepared weapons of death, he has his flaming arrows ready.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
See how the wicked conceive evil! They are pregnant with trouble. They give birth to dishonesty.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
They dig a deep hole to catch people, but then fall into it themselves.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
The trouble they cause rebounds to hit them on the head; their violence against others comes down on their own skulls.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will thank the Lord because he does what is right; I will sing praises to the name of the Lord Most High.