< Zabura 7 >
1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Tužaljka. Davidova. Ispjeva je Jahvi zbog Kuša Benjaminovca. O Jahve, Bože moj, tebi se utječem, od svih progonitelja spasi me, oslobodi,
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
da mi dušu ne zgrabe kao lav što razdire, a nema tko da izbavi.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Jahve, Bože moj, ako to učinih, ako je nepravda na rukama mojim,
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
ako zlom uzvratih prijatelju, ili oplijenih nepravedna tužitelja:
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
neka mi dušmanin progoni dušu i zgrabi je, neka mi život u zemlju satre i jetru u prašinu baci.
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Ustani, Jahve, u svom gnjevu, digni se na bijes tlačitelja mojih. Probudi se! Sud mi sazovi!
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Neka te okruži skupština narodna, nad njom sjedni visoko!
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
O Jahve, dosudi mi pravo po pravosti mojoj i po nevinosti koja je u meni.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Dokrajči bezakonje zlotvora, pravedna podigni, pravedni Bože koji proničeš srca i bubrege.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Meni je štit Bog koji spasava čestita srca.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Bog je pravedan sudac, on povazdan prijeti:
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
ako se ne obrate, mač će naoštriti, luk će svoj zapet' i pravo smjerit'.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
Spremit će za njih smrtonosno oružje, strijele će svoje užariti.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Eto, zlotvor zače nepravdu, otrudnje pakošću i podlost rodi.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Iskopa jamu i prodube; sam u jamu svoju pade!
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Pakost će njegova pasti njemu na glavu, njemu na tjeme okrenut se nasilje njegovo.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
A ja ću hvaliti Jahvu zbog pravde njegove i pjevat ću imenu Jahve višnjega.