< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Müzik şefi için - “Zambaklar” makamında - Davut'un mezmuru Kurtar beni, ey Tanrı, Sular boyuma ulaştı.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Dipsiz batağa gömülüyorum, Basacak yer yok. Derin sulara battım, Sellere kapıldım.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Tükendim feryat etmekten, Boğazım kurudu; Gözlerimin feri sönüyor Tanrım'ı beklemekten.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Yok yere benden nefret edenler Saçlarımdan daha çok. Kalabalıktır canıma kasteden haksız düşmanlarım. Çalmadığım malı nasıl geri verebilirim?
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Akılsızlığımı biliyorsun, ey Tanrı, Suçlarım senden gizli değil.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Ya Rab, Her Şeye Egemen RAB, Utanmasın sana umut bağlayanlar benim yüzümden! Ey İsrail'in Tanrısı, Benim yüzümden sana yönelenler rezil olmasın!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Senin uğruna hakarete katlandım, Utanç kapladı yüzümü.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Kardeşlerime yabancı, Annemin öz oğullarına uzak kaldım.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Çünkü evin için gösterdiğim gayret beni yiyip bitirdi, Sana edilen hakaretlere ben uğradım.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Oruç tutup ağlayınca, Yine hakarete uğradım.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Çula büründüğüm zaman Alay konusu oldum.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Kent kapısında oturanlar beni çekiştiriyor, Sarhoşların türküsü oldum.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Ama benim duam sanadır, ya RAB. Ey Tanrı, sevginin bolluğuyla, Güvenilir kurtarışınla uygun gördüğünde Yanıtla beni.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Beni çamurdan kurtar, İzin verme batmama; Benden nefret edenlerden, Derin sulardan kurtulayım.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Seller beni sürüklemesin, Engin beni yutmasın, Ölüm çukuru ağzını üstüme kapamasın.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Yanıt ver bana, ya RAB, Çünkü sevgin iyidir. Yüzünü çevir bana büyük merhametinle!
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Kulundan yüzünü gizleme, Çünkü sıkıntıdayım, hemen yanıtla beni!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Yaklaş bana, kurtar canımı, Al başımdan düşmanlarımı.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Bana nasıl hakaret edildiğini, Utandığımı, rezil olduğumu biliyorsun; Düşmanlarımın hepsi senin önünde.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Hakaret kalbimi kırdı, dertliyim, Acılarımı paylaşacak birini bekledim, çıkmadı, Avutacak birini aradım, bulamadım.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Yiyeceğime zehir kattılar, Sirke içirdiler susadığımda.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Önlerindeki sofra tuzak olsun onlara, Yandaşları için kapan olsun!
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Gözleri kararsın, göremesinler! Bellerini hep bükük tut!
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Gazabını yağdır üzerlerine, Öfkenin ateşi yapışsın yakalarına!
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Issız kalsın konakları, Çadırlarında oturan olmasın!
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Çünkü senin vurduğun insanlara zulmediyor, Yaraladığın insanların acısını konuşuyorlar.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Ceza yağdır başlarına, Senin tarafından aklanmasınlar!
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Yaşam kitabından silinsin adları, Doğrularla yan yana yazılmasınlar!
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Bense ezilmiş ve kederliyim, Senin kurtarışın, ey Tanrı, bana bir kale olsun!
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Tanrı'nın adını ezgilerle öveceğim, Şükranlarımla O'nu yücelteceğim.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
RAB'bi bir öküzden, Boynuzlu, tırnaklı bir boğadan Daha çok hoşnut eder bu.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Mazlumlar bunu görünce sevinsin, Ey Tanrı'ya yönelen sizler, yüreğiniz canlansın.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Çünkü RAB yoksulları işitir, Kendi tutsak halkını hor görmez.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
O'na övgüler sunun, ey yer, gök, Denizler ve onlardaki bütün canlılar!
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Çünkü Tanrı Siyon'u kurtaracak, Yahuda kentlerini onaracak; Halk oraya yerleşip sahibi olacak.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Kullarının çocukları orayı miras alacak, O'nun adını sevenler orada oturacak.

< Zabura 69 >