< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Sé mi salvador, oh Dios; porque las aguas han llegado, hasta mi cuello.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Mis pies están profundos en la tierra suave, donde no tengo donde apoyar los pies; He venido a aguas profundas, las olas están fluyendo sobre mí.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Estoy cansado de mi llanto; mi garganta está ardiendo: mis ojos se desperdician esperando a mi Dios.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Los que me odian sin causa son más numerosos que los pelos de mi cabeza; aquellos que están en mi contra, falsamente deseando mi destrucción, son muy fuertes; Devolví lo que no me habían quitado.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Oh Dios, ves cuán tonto soy; y mi maldad es clara para ti.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Los que tienen esperanza en ti, no sean avergonzados por mí, oh Jehová Dios de los ejércitos; no sean abatidos por mí los que esperan, oh Dios de Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Por tu amor he soportado ofensas; he sido avergonzado.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Me he vuelto extraño para mis hermanos, y como un hombre de un país lejano para los hijos de mi madre.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Estoy ardiendo con pasión por tu casa; y los insultos que han dicho de ti han venido sobre mí.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Mi amargo llanto y mi falta de alimento se convirtieron en vergüenza.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Cuando me puse la ropa de luto, dijeron mal de mí.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Soy motivo de admiración para los que tienen autoridad; una canción para aquellos que son dados a la bebida fuerte.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Pero en cuanto a mí, permíteme orar, oh Señor, en un momento cuando estés complacido; Oh Dios, dame una respuesta en tu gran misericordia, porque tu salvación es segura.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Llévame de las garras del lodo, para que no pueda descender a ella; déjame ser levantado de las aguas profundas.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
No me dejes cubrir por las aguas corrientes; no permitas que las aguas profundas pasen por mi cabeza, y no me dejes encerrar en el inframundo.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Da una respuesta a mis palabras, oh Señor; porque tu misericordia es buena: no escondas de tu siervo tu rostro.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
No me rechaces, porque estoy en problemas; rápidamente dame una respuesta.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Acércate a mi alma, para su salvación: sé mi salvador, por los que están contra mí.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Has visto mi vergüenza, cómo se burlaban de mí y menospreciaron; mis enemigos están todos ante ti.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Mi corazón se rompe con las ofensas, estoy lleno de dolor; Hice una búsqueda para que algunos se apiadaran de mí, pero no había nadie; No tenía quién me consolará.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ellos me dieron hiel por mi comida; y vino amargo para mi bebida.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Dejen que su mesa delante de ellos sea para su destrucción; deja que sus fiestas se conviertan en una trampa para ellos.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Sean cegados sus ojos para que no vean; deja que sus cuerpos estén temblando para siempre.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Deja que tu maldición venga sobre ellos; deja que el calor de tu ira los alcance.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Da sus casas a la destrucción, y no haya nadie en sus tiendas.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Porque son crueles con aquel contra quien está vuelta tu mano; hacen amarga la pena de aquel que es herido por ti.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Su castigo se incremente; que no entren en tu justicia.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Sean quitados sus nombres del libro de los vivientes, que no se numeren con los justos.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Pero yo soy pobre y estoy lleno de tristeza; déjame ser levantado por tu salvación, oh Señor.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Alabaré el nombre de Dios con una canción; Le daré gloria por lo que ha hecho.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Esto será más agradable al Señor que un buey o un becerro de pleno crecimiento.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Los pobres lo verán y se alegrarán: ustedes que son amantes de Dios, dejen que sus corazones tengan vida.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Porque los oídos del Señor están abiertos a los pobres, y él piensa en sus prisioneros.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Dejen que los cielos y la tierra lo alaben, los mares y todo lo que se mueve en ellos.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Porque Dios será el salvador de Sión y el edificador de las ciudades de Judá; para que pueda ser su lugar de descanso y herencia.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
La simiente de sus siervos tomará parte en ella, y allí descansan los amantes de su nombre.

< Zabura 69 >