< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Načelniku godbe na šestero strun, pesem Davidova. Reši me, Bog, ker vode mi prihajajo noter do duše,
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Pogrezam se v blato pregloboko; kjer ni trdnega pod nogo; zahajam v globočine vodâ; in val poplaveč me požira.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Trudim se vpijoč, suši se grlo moje; oči moje pešajo, ko upam v svojega Boga.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Več jih je ko glave moje lâs, ki me sovražijo po krivem; mogočneji so, ki me hočejo ubiti, ki so mi sovražniki po krivici; tedaj me silijo vrniti, česar nisem vzel.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O Bog, ti poznaš nespamet mojo, in krivice moje niso ti skrite.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Ne bodi jih mene sram, kateri čakajo tebe; Gospod, Bog vojnih krdél, rudečica naj ne oblije zaradi mene njih, ki iščejo tebe, Bog Izraelov.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Ker zavoljo tebe prenašam zasmehovanje; sramota pokriva obličje moje.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Tujec sem postal bratom svojim, in neznan matere moje sinovom.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Ker gorečnost za hišo tvojo me razjéda, in zasmehovanje njih, ki tebe zasmehujejo, mene zadeva.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Ko jokajoč pokorim s postom dušo svojo, tedaj se mi to šteje za najhujšo sramoto.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Ko se oblačim v raševino, tedaj sem jim v pregovor.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
O meni govoričijo vkup sedeči pri vratih, in pesmi pojó, ko pijejo opojno pijačo.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
O meni torej je prošnja moja tá do tebe, Gospod: čas je milosti, Bog, po obilnosti milosti svoje usliši me, po blagi zvestobi svoji.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Potegni me iz blata, in naj se ne pogreznem; otet naj bodem sovražnikov svojih, in iz globočin vodâ.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Valovje vodâ naj me poplaveč ne odnese, in globočina naj me ne pogoltne, in jama naj ne zapre ust svojih nad mano.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Usliši me, Gospod, ker dobra je milost tvoja; po obilosti usmiljenja svojega ozri se v mé.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
In ne skrivaj obličja svojega svojemu hlapcu; ker v stiski sem, hiti, usliši me!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Približaj se duši moji, ótmi jo; zavoljo sovražnikov mojih réši me.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Ti poznaš zasramovanje moje in mojo sramoto ter nečast mojo; pred teboj so vsi sovražniki moji.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Zasramovanje tare srce moje, tako da sem bolan; in ko ga čakam, da bi me miloval, nikogar ni; ali tolažiteljev, vendar ne najdem jih.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Dà, za živež mi dajó želča, in v žeji moji dajó mi piti octa.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Njih miza bodi pred njimi za zanko, in za povračila, za zadrgo.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Otemné naj njih oči, da ne vidijo; in daj, da ledja njih omahujejo neprestano.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Razlij na nje jezo svojo, in srd tvoj naj jih dohiti.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Pusti naj bodejo njih gradovi, v šatorih njih ne bodi prebivalca.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Ker preganjajo njega, kateregi si tí udaril, in po bolečini prebodencev tvojih spletajo pripovedke.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Pridevaj kazen kazni njih krivici, in naj ne pridejo v pravico tvojo.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Izbrišejo naj se iz življenja knjige, in s pravičnimi naj se ne zapisujejo.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Jaz pa ubožen in trpeč, blaginja tvoja, Bog, postavila me bode na višavo.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Hvalil bodem ime Božje s pesmijo, in poveličeval ga bodem sè zahvaljevanjem,
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Kar se bode bolje zdelo Gospodu, ko vol, junec rogat z razklanimi parklji.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Ko bodejo to videli krotki, veselili se bodo; in oživelo bode srce vaše, ki iščete Boga.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Ker Gospod se ozira na potrebne, in jetnikov svojih ne zameta.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Hvalila ga bodo nebesa in zemlja, morja in karkoli lazi po njih.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Ker Bog otima Sijon in zida z nova mesta Judovska, da stanujejo tam, in podedujejo ono deželo.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Nasledniki, pravim, hlapcev njegovih naj jo posedajo, in ljubitelji imena njegovega naj prebivajo v njej,

< Zabura 69 >