< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Ngisindisa, Nkulunkulu, ngoba amanzi asengene kuwo umphefumulo.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Ngiyatshona odakeni olujulileyo, lapho okungelakuma khona; ngingene emanzini atshonayo, lapho impophoma iyangicwilisa.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Ngidiniwe yikukhala kwami, umphimbo wami womile qha; amehlo ami ayafiphala ekulindeleni uNkulunkulu wami.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Abangizondayo ngeze banengi okwedlula inwele zekhanda lami; abangangibhubhisa, izitha zami ngaphandle kwecala, balamandla. Lokho engingakwebanga ngasengikubuyisela.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Nkulunkulu, wena uyabazi ubuthutha bami, lezono zami kazifihlakalanga kuwe.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Kabangayangeki ngenxa yami labo abakulindeleyo, Nkosi Jehova wamabandla; bangadunyazwa ngenxa yami labo abakudingayo, Nkulunkulu kaIsrayeli.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Ngoba ngenxa yakho ngithwele ihlazo; inhloni zisibekele ubuso bami.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Sengaba ngowemzini kubafowethu, lowezizweni kubantwana bakamama.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Ngoba ukutshisekela indlu yakho kungidlile, lenhlamba yabakuhlambazayo iwele phezu kwami.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Ngasengilila ekuzileni ukudla komphefumulo wami, njalo kwaba yikudunyazwa kimi.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Ngasengisenza isaka isembatho sami, ngaba yisiga kibo.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Abahlezi esangweni bakhuluma ngami, njalo ngaba yingoma yabanatha okunathwayo okulamandla.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Kodwa mina umkhuleko wami ukuwe, Nkosi, ngesikhathi somusa, Nkulunkulu, ngobunengi besihawu sakho, ngiphendule, ngeqiniso losindiso lwakho.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Ungophule odakeni, ngingatshoni; ngikhululwe kwabangizondayo lenzikini yamanzi.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Impophoma yamanzi kayingangicwilisi, lenziki ingangiginyi, lomgodi ungavali umlomo wawo phezu kwami.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Ngiphendula, Nkosi, ngoba uthandolomusa wakho lulungile; ngobunengi besihawu sakho uphendukele kimi.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Njalo ungayifihleli ubuso bakho inceku yakho; ngoba ngiyahlupheka, phangisa ungiphendule.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Sondela emphefumulweni wami, uwuhlenge, ungikhulule ngenxa yezitha zami.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Wena uyakwazi ukuthukwa kwami lehlazo lami lokudunyazwa kwami; izitha zami zonke ziphambi kwakho.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Ukuthukwa kuyidabule inhliziyo yami, njalo ngibuthakathaka. Bengilindele ongangihawukela, kodwa wayengekho, labaduduzayo, kodwa kangibatholanga.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Basebengipha inyongo ibe yikudla kwami, lekomeni kwami banginathisa iviniga.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Itafula labo eliphambi kwabo kalibe ngumjibila, ibe yisifu sabonwabileyo.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Amehlo abo kawafiphale ukuze bangaboni, njalo wenze inkalo zabo zihlale zithuthumele.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Thela intukuthelo yakho phezu kwabo, lolaka lwakho oluvuthayo lubafice.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Indawo yabo yokuhlala kayibe lunxiwa, kungabi khona ohlala emathenteni abo.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Ngoba omtshayileyo wena bayamzingela, njalo baxoxa kube buhlungu kwabalinyazwe nguwe.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Yengezelela ukona ekoneni kwabo, ukuze bangangeni ekulungeni kwakho.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Kabesulwe ogwalweni lwabaphilayo, bangabalwa kanye labalungileyo.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Kodwa mina ngilusizi, ngiyafuthelwa; usindiso lwakho, Nkulunkulu, kalungimise phezulu ngivikelekile.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Ngizadumisa ibizo likaNkulunkulu ngehubo, ngimkhulise ngokubonga.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Kuzakuba kuhle-ke eNkosini okwedlula inkabi kumbe ijongosi elilempondo lenklagu.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Abathobekileyo bazabona, bathokoze; lina elidinga uNkulunkulu inhliziyo yenu izaphila.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Ngoba iNkosi iyabezwa abaswelayo, njalo kayideleli izibotshwa zayo.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Kakuthi amazulu lomhlaba kuyidumise, izinlwandle lakho konke okunyakaza phakathi kwazo.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Ngoba uNkulunkulu uzasindisa iZiyoni, ayakhe imizi yakoJuda; njalo bahlale khona badle ilifa layo.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Lenzalo yenceku zakhe izakudla ilifa layo, labathanda ibizo lakhe bazahlala kuyo.

< Zabura 69 >