< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Kumqondisi wokuhlabela. Itshuni ethi, “Amaluba.” ElikaDavida. Ngisindisa, Oh Nkulunkulu, ngoba umsinga wamanzi usugamenxe ngentamo yami.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Ngiyagalula ezinzikini ezitotayo, lapho okungekho ndawo yokugxila. Sengifike enzikini; impophoma sezingikhulela.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Sengidiniwe yikumemeza ngicela uncedo; umphimbo wami usome qha. Amehlo ami aseze efiphele, edinga uNkulunkulu wami.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Labo abangizondayo kungelasizatho banengi okwedlula inwele zekhanda lami; banengi abayizitha zami kungelambangela, labo abafuna ukungidiliza. Ngiyaphoqelwa ukuhlawula engingakuntshontshanga.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Uyabazi ubuthutha bami, wena Nkulunkulu; isono sami kasifihlakalanga kuwe.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Akuthi labo abathemba kuwe bangayangiswa ngenxa yami, Oh Thixo, Thixo Somandla; akuthi labo abakudingayo, bangahlaziswa ngenxa yami, Oh Nkulunkulu ka-Israyeli.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Ngiyakubhensela ukugconwa ngenxa yakho, ihlazo lihuqiwe ebusweni bami.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Ngingowemzini kubafowethu, ngingowemzini emadodaneni kamama;
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
ngoba ukutshisekela indlu yakho kufuthelene kimi, lezethuko zalabo abakuthukayo ziwela kimi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Ngithi lapho ngilila ngizila ukudla, ngibhensele ukwetheswa inhlamba;
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
kuthi lapho ngivunula amasaka abantu badlale ngami.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Labo abalinda emasangweni bayangihleka, ngiyingoma nje yezidakwa.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Kodwa ngikhuleka kuwe, Oh Thixo, ngesikhathi somusa wakho; ngothando lwakho olukhulu, Oh Nkulunkulu, ngiphendula ngensindiso yakho eqinisekileyo.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Ngihlenga exhaphozini, ungangiyekeli ngigalule; ngikhulula kulabo abangizondayo, emanzini atshonayo.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Ungayekeli izikhukhula zingigalulise loba inziki zingiginye, loba umgodi uvaleke umlomo wawo phezu kwami.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Ngiphendula, Oh Thixo, ngenxa yokulunga kothando lwakho; emuseni wakho omkhulu phendukela kimi.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Ungayifihleli ubuso bakho inceku yakho; ngiphendula masinyane, ngoba ngiphakathi kohlupho.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Sondela ungikhulule; ngihlenga ngenxa yezitha zami.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Uyakwazi ukuthi ngigconwa njani, ngihlaziswa njalo ngiyangiswa; zonke izitha zami ziphambi kwakho.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Ukugconwa sekuyephule inhliziyo yami kwangitshiya esithubeni; ngadinga uzwelo ngaluswela, abaduduzi, kodwa ngabaswela.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Bathela inyongo ekudleni kwami banginathisa iviniga nxa ngomile.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Sengathi itafula eliphambi kwabo lingaba ngumjibila; sengathi lingaba yisijeziso lesithiyo.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Sengathi amehlo abo angafiphala ukuze bangaboni, lamaqolo abo akhokhobe kokuphela.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Thululela ulaka lwakho phezu kwabo; akuthi ulaka lwakho olwesabekayo lubehlele.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Sengathi indawo yabo ingaba ngamanxiwa; akungabi lamuntu ozahlala emathenteni abo.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Ngoba bahlupha labo obalimazayo bakhulume ngobuhlungu balabo obalimazayo.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Bethese amacala phezu kwamacala; ungayekeli bazuze isabelo sensindiso yakho.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Sengathi bangesulwa encwadini yokuphila bangaze babalwa kanye labalungileyo.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Ngisebuhlungwini, ngikhathazekile; sengathi insindiso yakho, Oh Nkulunkulu ingangivikela.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Ngizalidumisa ibizo likaNkulunkulu ngengoma, ngilibabaze ngokubonga.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Lokhu kuzamthabisa uThixo okwedlula inkabi, okwedlula inkunzi yonke ilempondo lamangqina ayo.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Abayanga bazabona bajabule lina elimdingayo uNkulunkulu, sengathi inhliziyo zenu zingaphila!
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
UThixo uyabezwa abaswelayo, kabeyisi abantu bakhe abathunjiweyo.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Akuthi izulu lomhlaba kumdumise, inlwandle lakho konke okunyakaza kuzo,
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
ngoba uNkulunkulu uzayisindisa iZiyoni ayakhe kutsha imizi yakoJuda. Yikhona-ke abantu bazakwakha khona balithathe libe ngelabo;
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
abantwana bezinceku zayo lizakuba yilifa labo, labalithandayo ibizo lakhe bazahlala khona.

< Zabura 69 >