< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Psalmus David, in finem, pro iis, qui commutabuntur. Salvum me fac Deus: quoniam intraverunt aquae usque ad animam meam.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Infixus sum in limo profundi: et non est substantia. Veni in altitudinem maris: et tempestas demersit me.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Laboravi clamans, raucae factae sunt fauces meae: defecerunt oculi mei, dum spero in Deum meum.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Multiplicati sunt super capillos capitis mei, qui oderunt me gratis. Confortati sunt qui persecuti sunt me inimici mei iniuste: quae non rapui, tunc exolvebam.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Deus tu scis insipientiam meam: et delicta mea a te non sunt abscondita.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Non erubescant in me qui expectant te Domine, Domine virtutum. Non confundantur super me qui quaerunt te, Deus Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Quoniam propter te sustinui opprobrium: operuit confusio faciem meam.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Extraneus factus sum fratribus meis, et peregrinus filiis matris meae.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Quoniam zelus domus tuae comedit me: et opprobria exprobrantium tibi, ceciderunt super me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Et operui in ieiunio animam meam: et factum est in opprobrium mihi.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Et posui vestimentum meum cilicium: et factus sum illis in parabolam.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Adversum me loquebantur qui sedebant in porta: et in me psallebant qui bibebant vinum.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Ego vero orationem meam ad te Domine: tempus beneplaciti Deus. In multitudine misericordiae tuae exaudi me, in veritate salutis tuae:
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Eripe me de luto, ut non infigar: libera me ab iis, qui oderunt me, et de profundis aquarum.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Non me demergat tempestas aquae, neque absorbeat me profundum: neque urgeat super me puteus os suum.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Exaudi me Domine, quoniam benigna est misericordia tua: secundum multitudinem miserationum tuarum respice in me.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Et ne avertas faciem tuam a puero tuo: quoniam tribulor, velociter exaudi me.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Intende animae meae, et libera eam: propter inimicos meos eripe me.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Tu scis improperium meum, et confusionem meam, et reverentiam meam.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
In conspectu tuo sunt omnes qui tribulant me, improperium expectavit cor meum et miseriam. Et sustinui qui simul contristaretur, et non fuit: et qui consolaretur, et non inveni.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Et dederunt in escam meam fel: et in siti mea potaverunt me aceto.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Fiat mensa eorum coram ipsis in laqueum, et in retributiones, et in scandalum.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Obscurentur oculi eorum ne videant: et dorsum eorum semper incurva.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Effunde super eos iram tuam: et furor irae tuae comprehendat eos.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Fiat habitatio eorum deserta: et in tabernaculis eorum non sit qui inhabitet.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Quoniam quem tu percussisti, persecuti sunt: et super dolorem vulnerum meorum addiderunt.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Appone iniquitatem super iniquitatem eorum: et non intrent in iustitiam tuam.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Deleantur de Libro viventium: et cum iustis non scribantur.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Ego sum pauper et dolens: salus tua Deus suscepit me.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Laudabo nomen Dei cum cantico: et magnificabo eum in laude:
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Et placebit Deo super vitulum novellum: cornua producentem et ungulas.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Videant pauperes et laetentur: quaerite Deum, et vivet anima vestra:
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Quoniam exaudivit pauperes Dominus: et vinctos suos non despexit.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Laudent illum caeli et terra, mare, et omnia reptilia in eis.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Quoniam Deus salvam faciet Sion: et aedificabuntur civitates Iuda. Et inhabitabunt ibi, et hereditate acquirent eam.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Et semen servorum eius possidebit eam, et qui diligunt nomen eius, habitabunt in ea.

< Zabura 69 >