< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Pour la fin, pour ceux qui seront changés, par David. Sauvez-moi, ô Dieu, parce que des eaux sont entrées dans mon âme.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Je suis enfoncé dans une boue profonde et sans consistance. Je suis venu dans la profondeur de la mer, et une tempête m’a submergé.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Je me suis fatigué en criant, ma gorge est devenue enrouée: mes yeux défaillent, pendant que j’espère en mon Dieu.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Ils se sont multipliés plus que les cheveux de ma tête, ceux qui me haïssent sans sujet. Ils se sont fortifiés, ceux qui me persécutent injustement; ce que je n’avais pas pris, je l’ai pourtant payé.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Ô Dieu, c’est vous qui savez ma folie; et mes péchés ne vous sont point cachés.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Qu’ils ne rougissent pas à cause de moi, ceux qui vous attendent, Seigneur, Seigneur des armées. Qu’ils ne soient pas confondus à mon sujet, ceux qui vous cherchent, ô Dieu d’Israël.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Puisque c’est à cause de vous que j’ai souffert l’opprobre, et que la confusion a couvert ma face.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Je suis devenu étranger à mes frères, un inconnu aux fils de ma mère.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Parce que le zèle de votre maison m’a dévoré, et que les outrages de ceux qui vous insultaient sont tombés sur moi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
J’ai couvert mon âme dans le jeûne, et on m’en a fait un sujet d’opprobre.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Et j’ai pris pour mon vêtement un cilice, et je suis devenu pour eux un proverbe.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Ceux qui étaient assis à la porte de la ville parlaient contre moi, et ceux qui buvaient du vin me chantaient en dérision.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Pour moi, je vous adresse ma prière, Seigneur; c’est le temps de votre bienveillance, ô Dieu.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Retirez-moi de la fange, afin que je n’y demeure pas enfoncé; délivrez-moi de ceux qui me haïssent, et du fond des eaux.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Qu’une tempête d’eau ne me submerge pas, qu’un abîme ne m’engloutisse pas; qu’un puits ne referme pas sa bouche sur moi.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Exaucez-moi, Seigneur, parce que votre miséricorde est bienfaisante; selon la multitude de vos bontés, jetez un regard sur moi.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Et ne détournez pas votre face de votre serviteur; parce que je suis tourmenté, exaucez-moi promptement,
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Soyez attentif à mon âme et délivrez-la à cause de mes ennemis: sauvez-moi.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
C’est vous qui connaissez mon opprobre, ma confusion et ma retenue.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Ils sont en votre présence, tous ceux qui me tourmentent: mon cœur a attendu l’opprobre et la misère.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ils m’ont donné pour nourriture du fiel, et dans ma soif ils m’ont abreuvé de vinaigre.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Que leur table devienne devant eux un filet, et la punition qu’ils méritent, une pierre d’achoppement.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Que leur yeux s’obscurcissent, afin qu’ils ne voient point: et tenez leur dos toujours courbé.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Répandez sur eux votre colère, et que la fureur de votre colère les saisisse.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Que leur habitation devienne déserte, et que dans leurs tabernacles il n’y ait personne qui habite.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Parce qu’ils ont persécuté celui que vous-même vous avez frappé, et qu’ils ont ajouté à la douleur de mes plaies.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Mettez iniquité sur leur iniquité, et qu’ils n’entrent point dans votre justice.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Qu’ils soient effacés du livre des vivants, et qu’avec les justes ils ne soient point écrits.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Pour moi, je suis pauvre et souffrant; votre secours, ô mon Dieu, m’a soutenu.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Je louerai le nom du Seigneur par un cantique, je le glorifierai par ma louange.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Et cela sera plus agréable à Dieu qu’un jeune veau qui pousse ses cornes et ses ongles.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Que les pauvres voient et se réjouissent: cherchez Dieu et votre âme vivra;
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Parce que le Seigneur a exaucé les pauvres, il n’a pas méprisé ceux qui sont dans les liens.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Que les cieux le louent, ainsi que la terre, la mer et tous les reptiles qu’ils contiennent.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Parce que Dieu sauvera Sion, et que les cités de Juda seront rebâties.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Et la race des serviteurs de Dieu la possédera; et ceux qui aiment son nom y habiteront.

< Zabura 69 >