< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Psaume de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Sosannim. Délivre-moi, ô Dieu, car les eaux me sont entrées jusque dans l'âme.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Je suis enfoncé dans un bourbier profond, dans lequel il n'y a point où prendre pied; je suis entré au plus profond des eaux, et le fil des eaux se débordant, m'emporte.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Je suis las de crier, mon gosier en est asséché; mes yeux sont consumés pendant que j'attends après mon Dieu.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Ceux qui me haïssent sans cause, passent en nombre les cheveux de ma tête; ceux qui tâchent à me ruiner, et qui me sont ennemis à tort, se sont renforcés: j'ai alors rendu ce que je n'avais point ravi.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Ô Dieu! Tu connais ma folie, et mes fautes ne te sont point cachées.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Ô Seigneur Eternel des armées! que ceux qui se confient en toi, ne soient point rendus honteux à cause de moi; [et] que ceux qui te cherchent ne soient point confus à cause de moi, ô Dieu d'Israël!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Car pour l'amour de toi j'ai souffert l'opprobre, la honte a couvert mon visage.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Je suis devenu étranger à mes frères, et un homme de dehors aux enfants de ma mère.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Car le zèle de ta maison m'a rongé, et les outrages de ceux qui t'outrageaient sont tombés sur moi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Et j'ai pleuré en jeûnant: mais cela m'a été tourné en opprobre.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
J'ai aussi pris un sac pour vêtement, mais je leur ai été un sujet de raillerie.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Ceux qui sont assis à la porte discourent de moi, et je sers de chanson aux ivrognes.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Mais, pour moi, ma requête s'adresse à toi, ô Eternel! Il y a un temps de [ton] bon plaisir, ô Dieu! selon la grandeur de ta gratuité. Réponds-moi selon la vérité de ta délivrance.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Délivre-moi du bourbier, fais que je n'y enfonce point, et que je sois délivré de ceux qui me haïssent, et des eaux profondes.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Que le fil des eaux se débordant ne m'emporte point, et que le gouffre ne m'engloutisse point, et que le puits ne ferme point sa gueule sur moi.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Eternel! Exauce-moi, car ta gratuité est bonne; tourne la face vers moi selon la grandeur de tes compassions;
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Et ne cache point ta face arrière de ton serviteur, car je suis en détresse: hâte-toi, exauce-moi.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Approche-toi de mon âme, rachète-la; délivre-moi à cause de mes ennemis.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Tu connais toi-même mon opprobre, et ma honte, et mon ignominie; tous mes ennemis sont devant toi.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
L'opprobre m'a déchiré le cœur, et je suis languissant; j'ai attendu que quelqu'un eût compassion de moi, mais il n'y en a point eu: et j'ai attendu des consolateurs, mais je n'en ai point trouvé.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ils m'ont au contraire donné du fiel pour mon repas; et dans ma soif ils m'ont abreuvé de vinaigre.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Que leur table soit un filet tendu devant eux; et [que ce qui tend] à la prospérité [leur soit] en piège.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Que leurs yeux soient tellement obscurcis, qu'ils ne puissent point voir; et fais continuellement chanceler leurs reins.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Répands ton indignation sur eux, et que l'ardeur de ta colère les saisisse.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Que leur palais soit désolé, et qu'il n'y ait personne qui habite dans leurs tentes.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Car ils persécutent celui que tu avais frappé, et font leurs contes de la douleur de ceux que tu avais blessés.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Mets iniquité sur leur iniquité; et qu'ils n'entrent point en ta justice.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Qu'ils soient effacés du Livre de vie, et qu'ils ne soient point écrits avec les justes.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Mais pour moi, qui suis affligé, et dans la douleur, ta délivrance, ô Dieu! m'élèvera en une haute retraite.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Je louerai le Nom de Dieu par des Cantiques, et je le magnifierai par une louange solennelle.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Et cela plaira plus à l'Eternel qu'un taureau, plus qu'un veau qui a des cornes, et l'ongle divisé.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Les débonnaires le verront, [et] ils s'en réjouiront, et votre cœur vivra, [le cœur, dis-je, de vous tous] qui cherchez Dieu.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Car l'Eternel exauce les misérables, et ne méprise point ses prisonniers.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Que les cieux et la terre le louent; que la mer et tout ce qui se meut en elle le louent aussi.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Car Dieu délivrera Sion, et bâtira les villes de Juda; on y habitera, et on la possèdera.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Et la postérité de ses serviteurs l'héritera, et ceux qui aiment son Nom demeureront en elle.

< Zabura 69 >