< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Au chef des chantres. Sur les Chochanim. De David. Viens à mon secours, ô Dieu, car les flots m’ont atteint, menaçant mes jours.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Je suis plongé dans la vase d’un gouffre; pas un pouce de terrain pour y poser le pied! Je suis descendu dans des eaux profondes, et les vagues me submergent.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Je suis exténué à force de crier, ma gorge est enflammée, mes yeux sont éteints à force d’attendre l’aide de mon Dieu.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Plus nombreux que les cheveux de ma tête sont ceux qui me haïssent pour rien; puissants sont mes oppresseurs, qui me poursuivent de leur haine gratuite. Si je les avais lésés, déjà je leur aurais fait réparation.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O Dieu, tu serais instruit de ma folie, mes crimes ne te resteraient point cachés.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Qu’ils n’aient pas à rougir à cause de moi, ceux qui espèrent en toi, Seigneur, Eternel-Cebaot! Qu’ils ne soient pas couverts de confusion à mon sujet, ceux qui te recherchent, Dieu d’Israël!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Car c’est pour toi que je supporte les insultes, que la honte couvre mon visage.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Je suis devenu un étranger pour mes frères, un inconnu pour les fils de ma mère,
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
parce que le zèle pour ta maison me dévore, et que les insultes de tes blasphémateurs retombent sur moi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Je pleure tout en m’imposant le jeûne, et ceci même a tourné à opprobre pour moi.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
J’Ai endossé comme vêtement un cilice, et suis devenu pour eux un sujet de sarcasme.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Ceux qui sont assis aux portes déblatèrent contre moi, les buveurs de liqueurs fortes me chansonnent.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Toutefois, ma prière s’élève vers toi, Eternel, au moment propice; ô Dieu, dans ta bonté infinie, exauce-moi, en m’accordant ton aide fidèle.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Retire-moi du bourbier, pour que je n’y sombre pas; puissé-je être sauvé de mes ennemis et des eaux profondes!
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Ne permets pas que je sois submergé par la violence des flots, englouti par le gouffre; que la bouche de l’abîme ne se referme pas sur moi!
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Exauce-moi, Eternel, car précieuse est ta grâce; selon la grandeur de ta miséricorde, tourne-toi vers moi.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Ne dérobe point ta face à ton serviteur; car je suis dans la détresse, hâte-toi de m’exaucer.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Approche-toi de mon âme, sauve-la; à cause de mes ennemis, tire-moi du danger.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Tu connais, toi, mon opprobre, ma honte, ma confusion; tous mes persécuteurs sont là devant toi.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
La honte a brisé mon cœur, j’en suis au désespoir; j’attends qu’on me plaigne, mais c’est en vain; qu’il me vienne des consolateurs: je n’en trouve point.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Dans mes aliments, ils mettent du poison; pour apaiser ma soif, ils m’abreuvent de vinaigre.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Que la table dressée devant eux leur devienne un piège, qu’elle soit un traquenard pour ces gens heureux!
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Que leurs yeux s’assombrissent, perdent la vue! Fais vaciller sans cesse leurs reins.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Déverse sur eux ton courroux, que ton ardente colère les accable!
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Que leur demeure devienne une ruine, que dans leurs tentes il ne reste plus un habitant!
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Car ils s’acharnent contre celui que tu as frappé, et se plaisent à gloser sur les maux de tes victimes.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Mets donc à leur compte crime sur crime; qu’ils ne soient point admis à se justifier devant toi!
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Qu’ils soient effacés du livre des vivants, et que parmi les justes ils ne soient point inscrits!
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Mais moi, si malheureux et si souffrant, ton secours, ô Dieu, est ma protection.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Je veux célébrer le nom de Dieu par des cantiques, et l’exalter par des actions de grâce,
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
plus agréables à l’Eternel qu’un taureau aux grandes cornes, aux puissants sabots.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
A cette vue, les humbles seront dans la joie; vous qui êtes en quête de Dieu, votre cœur se ranimera!
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Car l’Eternel prête l’oreille aux malheureux, et ses captifs, il ne les dédaigne point.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Que le ciel et la terre le glorifient, les mers et tout ce qui s’y meut!
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Car Dieu viendra au secours de Sion: il rebâtira les villes de Juda; on s’y établira et on en prendra possession.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
C’Est la postérité de ses serviteurs qui les aura en héritage; ceux qui aiment son nom y fixeront leur demeure.

< Zabura 69 >