< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Au chef de musique. Sur Shoshannim. De David. Sauve-moi, ô Dieu! car les eaux [me] sont entrées jusque dans l’âme.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Je suis enfoncé dans une boue profonde, et il n’y a pas où prendre pied; je suis entré dans la profondeur des eaux, et le courant me submerge.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Je suis las de crier; mon gosier est desséché; mes yeux se consument, pendant que j’attends mon Dieu.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Ceux qui me haïssent sans cause sont plus nombreux que les cheveux de ma tête; ceux qui voudraient me perdre, qui sont à tort mes ennemis, sont puissants; ce que je n’avais pas ravi, je l’ai alors rendu.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Ô Dieu! tu connais ma folie, et mes fautes ne te sont pas cachées.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Que ceux qui s’attendent à toi ne soient pas rendus honteux à cause de moi, Seigneur, Éternel des armées! Que ceux qui te cherchent ne soient pas rendus confus à cause de moi, ô Dieu d’Israël!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Car à cause de toi j’ai porté l’opprobre, la confusion a couvert mon visage.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Je suis devenu un étranger à mes frères, et un inconnu aux fils de ma mère;
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Car le zèle de ta maison m’a dévoré, et les outrages de ceux qui t’outragent sont tombés sur moi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Et j’ai pleuré, mon âme était dans le jeûne; et cela m’a été en opprobre.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
J’ai pris aussi un sac pour mon vêtement, et je leur suis devenu un proverbe.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Ceux qui sont assis dans la porte parlent contre moi, et je sers de chanson aux buveurs.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Mais, pour moi, ma prière s’adresse à toi, Éternel, en un temps agréé. – Ô Dieu! selon la grandeur de ta bonté, réponds-moi selon la vérité de ton salut.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Délivre-moi du bourbier, et que je n’y enfonce point; que je sois délivré de ceux qui me haïssent et des profondeurs des eaux.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Que le courant des eaux ne me submerge pas, et que la profondeur ne m’engloutisse pas, et que le puits ne ferme pas sa gueule sur moi.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Réponds-moi, ô Éternel! car ta gratuité est bonne; selon la grandeur de tes compassions, tourne-toi vers moi;
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Et ne cache pas ta face de ton serviteur, car je suis en détresse. Hâte-toi, réponds-moi.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Approche-toi de mon âme, sois son rédempteur; rachète-moi à cause de mes ennemis.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Toi, tu connais mon opprobre, et ma honte, et ma confusion: tous mes adversaires sont devant toi.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
L’opprobre m’a brisé le cœur, et je suis accablé; et j’ai attendu que [quelqu’un] ait compassion [de moi], mais il n’y a eu personne, … et des consolateurs, mais je n’en ai pas trouvé.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ils ont mis du fiel dans ma nourriture, et, dans ma soif, ils m’ont abreuvé de vinaigre.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Que leur table soit un piège devant eux, et que ce qui tend à la prospérité leur soit un filet;
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Que leurs yeux soient obscurcis de sorte qu’ils ne voient pas, et fais continuellement chanceler leurs reins.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Répands sur eux ton indignation, et que l’ardeur de ta colère les atteigne.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Que leur demeure soit désolée, qu’il n’y ait personne qui habite dans leurs tentes.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Car ils persécutent celui que toi tu as frappé, et parlent pour la douleur de ceux que tu as blessés.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Mets iniquité sur leur iniquité, et qu’ils n’entrent pas en ta justice;
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Qu’ils soient effacés du livre de vie, et qu’ils ne soient pas inscrits avec les justes.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Mais pour moi, je suis affligé et dans la douleur: que ton salut, ô Dieu, m’élève en un lieu de sûreté!
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Je louerai le nom de Dieu dans un cantique, et je le magnifierai par ma louange;
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Et cela plaira plus à l’Éternel qu’un taureau, un bœuf qui a des cornes et l’ongle divisé.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Les débonnaires le verront, ils se réjouiront; vous qui cherchez Dieu, votre cœur vivra.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Car l’Éternel écoute les pauvres, et ne méprise pas ses prisonniers.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Les cieux et la terre le loueront, les mers et tout ce qui se meut en elles.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Car Dieu sauvera Sion, et bâtira les villes de Juda; et on y habitera, et on la possédera;
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Et la semence de ses serviteurs l’héritera, et ceux qui aiment son nom y demeureront.

< Zabura 69 >