< Zabura 69 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
To the Chief Musician. On "The Lilies." David’s. Save me, O God, For waters have entered as far as the life;
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
I have sunk in deep swamp, Where there is no place to stand, I have come into abysses of waters, Where a flood hath overflowed me;
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
I am weary with mine outcry, Parched is my throat, —Mine eyes have become dim, through waiting for my God.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
More than the hairs of my head, Are they who hate me without cause, —Firmer than my bones, Are they who are my foes for false cause, —What I had not plundered, then, had I to restore.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O God, thou, hast known my folly, And, my wrong-doings, from thee, have not been hid.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Let them not be ashamed, through me, Who have waited for thee, O My Lord, Yahweh of hosts, —Let them not be confounded, through me, Who are seeking thee, O God of Israel!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Because, for thy sake, have I borne reproach, Confusion hath covered my face;
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
One estranged, have I become, to my own brethren, Yea, an alien, to the sons of my own mother;
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Because, zeal for thy house, hath eaten me up, And, the reproaches of them who have reproached thee, have fallen upon me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
When I have humbled my soul with fasting, Then hath it turned to my reproach;
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
When I have made my clothing of sackcloth, Then have I served them for a by-word;
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
They who sit in the gate talk against me, —And [against me are] the songs of them who imbibe strong drink.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
But, as for me, my prayer shall be unto thee, O Yahweh, in a time of acceptance, O God, in the abounding of thy lovingkindness, answer me with thy saving faithfulness.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Rescue me out of the mire, lest I sink, Let me be rescued, From my haters, and, From abysses of waters:
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Let not a flood of waters overflow me, And let not the depth swallow me up, Neither let the well close, over me, her mouth.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Answer me, O Yahweh, for good is thy lovingkindness, According to the abounding of thy compassions, turn thou towards me:
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Then do not hide thy face from thy servant, Because I am in distress, haste thou—answer me!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Oh draw near unto my soul—redeem it, Because of mine enemies, ransom me.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Thou, knowest my reproach, and my shame, and my confusion, Before thee, are all mine adversaries.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Reproach hath broken my heart, and I am weak, —Though I waited for one to pity me, yet there was none, And for comforters, yet I found not any.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
But they put in my food—poison! And, for my thirst, they gave for my drink—vinegar!
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Let their table, before them, become a snare, And unto their friends, a lure;
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Let their eyes become too dim to see, And, their loins, continually cause thou to shake;
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Pour out over them thine indignation, And let, the glow of thine anger, overtake them:
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Let their encampment become desolate, In their tents, be there none to dwell:
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
For, whom, thou thyself, hadst smitten, they pursued, And, unto the pain of thy wounded ones, they must needs add.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Lay punishment on their iniquity, And let them not enter into thy righteousness;
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Let them be blotted out of the book of life, And, with the righteous, let them not be enrolled.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
I, then, am humbled and in pain, Thy salvation, O God, may it set me on high.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
I will praise the Name of God with a song, And will magnify him with thanksgiving;
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
So shall it be more pleasing to Yahweh than a bullock of the herd, Showing horn [and] divided hoof.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
The humbled have seen—they rejoice! Ye seekers of God, let your heart, then, revive;
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
For, a Hearkener to the needy, is Yahweh, And, his prisoners, hath he not despised.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Let the heavens and the earth, praise him, The seas, and everything that creepeth therein.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
For, God, will save Zion, And build the cities of Judah, So shall men dwell there, and possess it:
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Yea, the seed of his servants, shall inherit it, And, the lovers of his Name, shall settle down therein.