< Zabura 69 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
For the leader. On shoshannim. Of David. Save me, O God; for the waters are threatening my life.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
I am sunk in depths of mire, where ground there is none. I am come into deep deep waters, the flood overwhelms me.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
I am weary of crying, my throat is parched, my eyes are wasted with waiting for God.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
More than the hairs of my head are those who wantonly hate me. More than my bones in number are those who are falsely my foes. That which I never robbed, how am I then to restore?
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O God, you know my folly, my guilt is not hidden from you.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Through me let not any be shamed, who wait for you, Lord God of hosts. Through me let not those be confounded who seek you, O God of Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
It’s in your cause that I have borne taunts, and my face has been covered with shame;
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
I became to my kindred a foreigner, to my mother’s sons a stranger.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
It was zeal for your house that consumed me, and the insults they hurled at you fell upon me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
When I chastened myself with fasting, they took occasion to taunt me.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
When I put on a garment of sackcloth, they made me the theme of a taunt-song.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Those who sit in the gate make sport of me in the music of drunken songs.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
But I pray to you, Lord, for a time of favour. In your great love answer me; with your loyal help, save me
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
from sinking down in the mire. Lift me out of the deep deep waters,
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
that the rushing flood may not drown me, that the deep may not swallow me up, nor the pit close her mouth upon me.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Answer me, Lord, in your gracious kindness, turn to me in your great compassion.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Hide not your face from your servant, for I am in trouble; O answer me speedily.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Draw near to me, redeem me; because of my enemies, ransom me.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
You know how I am insulted; in your sight are all my foes.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Insult has broken my heart, past cure are my shame and confusion. For pity I looked – there was none! And for comforters, but I found none.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Poison they gave me for food, and to slake my thirst they gave vinegar.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
May their table, outspread, be a trap to them, and their peace-offerings be a snare.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
May their eyes be darkened and blind, make them shake without ceasing.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Pour your indignation upon them, let your burning wrath overtake them.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
May their camp be a desolation, in their tents be there none to live.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
For those whom you struck, they persecute, and those whom you wounded, they pain yet more.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Charge them with sin upon sin, may they not be acquitted by you.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
From the book of life be they blotted, may their names not be written with the righteous.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Lift me, O God, by your help above my pain and misery.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Then will I praise God in song and magnify him with thanksgiving,
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
which shall please the Lord better than ox, or than bullock with horns and hoofs.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
The oppressed shall rejoice at the sight. You who seek after God, let your heart revive.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
For the Lord listens to the poor, he does not despise his prisoners.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Let the heavens and the earth sing his praises, the seas, and all creatures that move in them.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
For God will bring help to Zion, and build up the cities of Judah, his people shall live there in possession.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
His servants’ children shall have it for heritage, and those who love him shall live therein.