< Zabura 69 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
“To the chief musician upon Shoshannim, by David.” Save me, O God; for the waters are come even to threaten my life.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
I am sunk in the mire of the deep, where there is no standing; I am come into the depths of the waters, and the flood overfloweth me.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
I am weary of my calling; my throat is hoarse; my eyes fail, while I hope for my God.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
More than the hairs of my head are those that hate me without a cause; numerous are those that would destroy me, that are my enemies wrongfully: what I have not robbed shall I now restore.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O God, thou art well aware of my folly, and my guilty deeds are from thee not hidden.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Let not those that wait on thee, O Lord Eternal of hosts, be made ashamed through me: let not those that seek thee be confounded through me, O God of Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Because for thy sake have I borne reproach, hath confusion covered my face.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
A stranger am I become unto my brothers, and an alien unto my mother's children.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Because the zeal for thy house hath devoured me; and the reproaches of those that reproached thee are fallen upon me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
When I wept at the fasting of my soul, it became a reproach to me.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
And when I made sackcloth my garment, I became a proverb to them.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Those that sit in the gate talk against me; and [about me make] songs the drinkers of strong drink.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
But as for me, I direct my prayer unto thee, O Lord, in a time of favor; O God, in the multitude of thy kindness: answer me in the truth of thy salvation.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Deliver me out of the mire, that I may not sink: let me be delivered from those that hate me, and out of the depths of the waters.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Let not the flood of waters overflow me, and let not the deep swallow me up, and let not the pit close its mouth upon me.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Answer me, O Lord; for thy kindness is good: according to the multitude of thy mercies turn thou unto me.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
And hide not thy face from thy servant; for I am in distress: make haste and answer me.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Draw nigh unto my soul, and redeem it: because of my enemies do thou ransom me.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Thou well knowest my reproach, and my shame, and my confusion: before thee are all my assailants.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Reproach hath broken my heart; and I am sick; and I waited for pity, but there was none; and for comforters, but I found none.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
And they put into my food gall; and in my thirst they give me vinegar to drink.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
May [then] their table become a snare before them: and to those that are at peace, a trap.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
May their eyes become dark, that they cannot see; and make their loins continually to waver.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Pour out over them thy indignation, and let the heat of thy anger overtake them.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
May their palace become desolate: in their tents let no one dwell.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
For whom thou hast smitten they persecute; and of the pain of those whom thou but wounded do they converse.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Lay guilt upon their guilt; and let them not come into thy righteousness.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Let them be blotted out of the book of the living; and with the righteous let them not be written down.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
But I am poor and suffering: let thy salvation, O God, set me up on high.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
I will praise the name of God with song, and will magnify him with thanksgiving.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
And this will please the Lord better than an ox or bullock having horns and cloven hoofs.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
The meek will see this, and be rejoiced: ye that seek God, and your heart shall revive.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
For the Lord listeneth unto the needy, and his prisoners he despiseth not.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Let heaven and earth praise him, the seas, and every thing that moveth therein.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
For God will save Zion, and will build the cities of Judah: that they may abide there, and have it in possession:
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
And the seed of his servants shall inherit it; and they that love his name shall dwell therein.